Karyace maras tushe da wasu ke yadawa cewa darakta mai kula da fasahar sadarwar zamani a hukumar zabe ta kasa ya ajiye aikinsa sakamakon takaddamar da akeyi na mallakar rumbun tara bayanai na zamani wato “SERVER”

Hukumar tace Mr Chidi Nwafor yananan akan aikinsa, kwanannan ma shi da wasu jami’an hukumar suka dawo daga kasar South Africa, inda suka halarci taron shekara-shekara wanda ya gudana 18 – 20 ga wannan wata na June.

Hukumar tayi kira ayi watsi da wannan jita-jita wacce bata da tushe balle makama.

Published by Ibrahim Ali Ahmed

Political Analyst

Leave a comment

Design a site like this with WordPress.com
Get started