
Daga: SANI ROGON AIKAWA DALA.
(Kalaman wani yaro da naji da kunnena)
Jiya Talata ina tsaye Daidai jakara Bola zan hau babur Din Adaidaita sahu, sai wani yazo saura mutum daya, amman Da wani yaro agaba yazauna gefen babur din hannunsa rike da kullun buhun Leda dakuma wani kwano, ban vata lokaciba na hau sai tafiya, Muna tafiya ina waya da wata mace, banyi auneba sai naga babu yarondake zaune agaba, nayi mamaki naceda mai adaidaita sahun ina kuma yaron dake zaune agaban mashin din naga yasauka bamu karasa inda zai saukaba, budar bakin mai adaidaita sahun sai yacemin “CEWA YAYI ASHIRINCE DASHI NIKUMA A TALATIN NAKE ZUWA” take naji wani bakin ciki ya cikamin zuciya, saboda bai kyautaba baisan wanne hali yaron yake cikiba, nace masa wallahi malam bakada imani, musulmine fa dan uwanka yaro, wanda baifi shekaru gomaba, shin naira gomace zatasa ka kasa taimakonsa ga kaya. Zuciyata cike da fushi na sauka daga kan Adaidaita sahun, nadawo akasa ina neman yaron, nafi minti goma ina nemansa ban ganshiba, zuciyata cikeda bakin ciki, kawai sai na fasa tafiya a dan sahun nabiyo ta lunguna da kafata, IKO SAI ALLAH, saura kadan in karasa sai na hangi yaron yanata sauri, duk saurina yafini sauri, duk fa wannan saurin da yakeyi kayane akansa, dakuma kwano a hannunsa, nayi sauri naje na tarar dashi, nace masa saurin me kake yaro?
ALLAHU AKBAR!!! HAWAYENE sharkaf a kan kuncinsa sunata zuba, tausayinsa ya kamani, nace masa shin ba kaine muka hau adaidaita sahu dakaiba a jakara?
yacemin nine, nace to mai yasaka kuka?
yacemin ina kukane saboda tun laasar nabaro gida, wannan Abincin kuma ummarmu da kannena suna jirana inkai musu suci! nace masa to a ina kake karvo abincin?
sai yacenun Abincin sadake daga Gidan HAJIYA MARIYA MAHAIFIYAR DANGOTE, Kullum sai naje na karvo saboda mahaifinmu ya mutu, kullum sai na shafe awanni biyu zuwa da dawowa akafata, sannan in hau mashin na naira ashirin zaman Gaba akaini gida!
take tausayinsa yakamani nace masa kayi hakuri wata rana sai labari yaro, ga mamakina sai naji yacemun “MALAM WALLAHI DUK SANDA NASAMU WATA DAMA SAI NA SHUKA RASHIN MUTUNCI SAI NA AIKATA RASHIN IMANI, SABODA AN RASA MASU TAUSAYA MANA!!!
take sai naji kwallah na neman zubomin a idanuna, nace masa kayi hakuri ba dukka mutane suka zama dayaba, muje gidan inga umman taku, nace masa!!! da muka fito titi, muka sake hawa wani mashin din har kusada kofar gidansu, muka sakko muka taka da kafarmu har kofar gidansu, wani abin tausayi uwar tana tsaye a soro yara biyu mace da namiji suna kuka kusa da ita, da Alama kukan yunwane, suna ganinmu suka rike kwanon dake hannun yayannnasu suka fara budewa, mahaifiyarsu bazata wuce shekaru talatin da biyarba, Amman wahalar rayuwa na neman tsofarda ita, cikin razana tacemun BAWAN ALLAH LAFIYA?
Allah yasadai lafiya, na kwashe labari na gaya mata, cikin tausayi tace wallahi badan wannan yaronba Abinci sai ya gagaremu, mahaifinsu ya rasu tsawon shekaru uku, Alumma sun gaza taimaka mana, yabarmu agidan Haya dakuma yara guda uku, basa zuwa makaranta, saboda halin rayuwa, kullum wannan yaron shike zuwa ya karvo mana sadakar Abinci.
babban abinda yabani mamaki, unguwar ga mawadata amman angaxa basu tallafi
munfi mintuna talatin muna tattaunawa da uwar, nayi Alkawarin dinka musu kayan makaranta tareda kaisu makarantar gamida yi mata alkawarin wasu abubuwa wanda nasan zan iya. na dauko dan abinda baxai gagaraba na mika musu, yaronnan yanata godiya uwar kuwa banda kuka babu Abinda takeyi, nace mata kiyi hakuri zan dinga zuwa lokaci zuwa lokaci, kiyi hakuri kada kidamu rayuwace wata rana sai labari.
“DARASIN DANA KOYA*
Da yawan mutane rashin agaxa musu shine yakesawa zuciyarsu ta qeqashe, yakamata mu dinga agazawa raunana, muma sai ubangiji ya agaxa mana, duk wanda ya nemi agaji mu agaxa masa rayiwace bamusan inda zamu tsinci kanmuba wallahi.
ubangiji ya agaxa mana.
You must be logged in to post a comment.