Kada Mu Sake Amincewa Da Su

#S4S2019

‘Yan Najeriya na bukatar shugabanni masu kishin kasa masu tabbatar da an maido da zaman lafiya arziki da cigaba da walwala, ba zamu amince da komawa gidan jiya ba musamman a hannun mutanen da suka maida kasar baya.

Kowa ya sani cewa, Jam’iyyar PDP ta fito fili ta nemi afuwar Al’ummar Najeriya saboda sunsan irin ta’adin da suka aikata a Gwamnatin su, domin kuwa bahause yace idan ba rami mai ya kawo rami?

Lokaci bai yi ba da Jam’iyyar PDP zasu komo domin neman darewa kan kujerar mulkin Najeriya a halin yanzu, bayan shekaru hudu (4) kacal da barin kujerar, sunyi shekaru gona sha shida (16) suna yin abinda suka ga dama.

Don haka ‘yan Najeriya ba zasu amince a sake sayar musu da kadarorin da suka mallaka ba, a wancan lokacin ma haka suka sayarwa da kawunansu dukkanin albarkatun Najeriya daga su sai ‘ya’yansu, yanzu kuma suna so su sake samun irin waccan damar su karasamu shikenan mu zama bayin turawa, su kuma su tafi can da iyalansu suci gaba da hole rayuwarsu.

Sanin kowane cewa, dan takarar PDP ya sha alwashin sayar da matatun mai da muke dasu, sannan yayiwa kungiyoyin masu luwadu da madigo alkawarin basu damar cin karansu ba babbaka, duk kuwa da cewa addinan Musulunci da na Kiristoci sun hadu domin yakar wannan dabi’a, inda suka ki yadda ayi dokar a baya domin bada dama ga irin wannan fitsara da turawa ke kokarin shigo mana da ita, sai gashi mai neman shugabancin kasar a tutar Jam’iyyar PDP yace susha kuruminsu indai ya hau kujera zai basu dama.

Ya zama wajibi ga Musulmi da Kiristoci mu hada karfi wajen yakar masu kokarin maida hannun agogo baya.

Daga Na’Allah Raheemeeb

Sojojin Najeriya Sun Karbi Umarnin Shugaban Kasa

#S4S2019

Kakakin sojojin Najeriya yasha alwashin yin biyayya ga Shugaban Kasa kuma babban kwamandan tsaro sau-da-kafa wajen aiwatar da umarnin da ya bayar game da masu satar akwatin zabe a yayin gudanar da zaben a Najeriya.

Kakakin sojojin Najeriya Sagir Musa yace, da zarar babban kwamanda ya bada oda sai aiwatarwa kawai batare da wani noke-noke ba ko yin wata tirjiya ga umarninsa.

Ya tabbatar wa jama’a cewa, sojojin za su fito ranar zabe, duk da dai ba zasu shiga gaban akwatin zabe ba amma za su tsaya daga baya-baya inji kakakin sojan Najeriya.

Daga Na’Allah Raheemeeb

Shugaban Jam’iyyar PDP Na Kasa Ya Zargi Buhari

#S4S2019

Shugaban Jam’iyyar PDP na Kasa Prince Uche Secondus yace Shugaban Kasa Buhari yana tunzura jami’an tsaro domin yin kwacen mulkin Kasar da taimakonsu, yace bai taba ganin Shugaban da yayi umarni a kashe Al’ummar kasa ba sai Buhari.

Zabe ba harka ce ta jami’an sojoji ba, don haka bai kamata ace soja ya shiga harkar zabe ba bayan ga ‘yan sanda, a cewar sa Shugaba Buhari ya daura yaki ne da ‘yan Najeriya tunda yayi umarni a kashe su.

Daga Na’Allah Raheemeeb

Jam’iyyar APC Ta Ja Kunnen Kasashen Turawa

#S4S2019

Jam’iyyar APC mai mulki Najeriya ta gargadi Kasashen Amurika, Buritaniya da sauran kasashen yankin turawa da su daina tsomawa Kasar baki a harkokin siyasarta.

Wannan ya fito daga bakin kakakin Jam’iyyar APC na Kasa Yekini Nabena, inda yace suma Kasashen turawan suji da nasu matsalolin dake addabarsu, inda ya kara da cewa a kowane zabe da Kasar Najeriya zata gudanar tanayin iyaka kokarin ta na bada dama ga turawan su shigo domin sa ido a wajen zaben ba tare da wata tsangwama ba.

Daga karshe yayi Allah wadai da yadda hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasar ta dage zaben da ta shirya gudanarwa Asabar 16/2/2019.

Daga Na’Allah Raheemeeb

Kalubale Ga Masu Satar Akwatin Zabe

#S4S2019

Shugaba Buhari yayi gargadin duk wanda ya saci akwatin zabe, yasani cewa, zai yi hakan ne a bakin ransa, ya ja kunnen jami’an tsaro daga kan soja zuwa ‘yan sanda kada su ragawa duk wanda yayi kokarin sace akwati ko kuma yin amfani da ‘yan daba wajen tada hankalin masu zabe.

Duk wanda yayi hakan ya tabbatar da zaiyi hakanne na karshe a rayuwarsa, shugaba Buhari yayi gargadin ne a yayin gudanar da wani taro na gaggawa na masu ruwa da tsaki da Jam’iyyar sa ta APC ta kira a babban ofishinsu dake Abuja.

Shugaban Kasar yace baya zaton za’a sami irin masu kokarin tada hankalin, amma duk wanda ya aikata hakan to ya kuka da kansa.

Daga Na’Allah Raheemeeb

Kungiyar Kwadago Ta Nemi Gwamnati Ta Bada Hutun Aiki

#S4S2019

Kungiyar kwadago a Najeriya ta bukaci Gwamnati ta bada hutu domin ma’aikata su sami damar yin tafiye-tafiye zuwa garuruwansu domin kada kuri’unsu, sakamakon dage zaben da hukumar zaben Kasar tayi.

Shugaban kungiyar kwadagon a Najeriya Comrade Ayuba Wabba yace basuji dadin dage zaben ba, kasancewar ma’aikata sunyi tafiye-tafiye mai nisa zuwa garuruwan nasu domin su yi zabe sai kuma gashi an dage zaben.

Daga Na’Allah Raheemeeb

Babu Wani Shiri Na Canja Shugaban Hukumar Zabe

#S4S2019

Shugaba Muhammad Buhari yace babu wani shiri na canja Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC

Wannan magana ta fito daga bakin kakakin shugaba Buhari ta kafafan hada labarai Mallam Garba Shehu.

Daga Na’Allah Raheemeeb

Hukumar Zaben Najeriya Ta Dauki Alhakin Dage Zabe

#S4S2019

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC ta tabbatarwa duniya cewa babu wanda yayi mata shisshigi wajen dage zaben Kasar da ta shirya gudanarwa Asabar 16/2/2019 kamar yadda shugabanta Prof. Yakubu Mahmood ya bayyana

Yace “hukumar ta dauki nauyin dage zaben dari-bisa-dari, ba domin anyi mata shisshigin ko katsalandan a harkokinta ba, haka kuma ba za ta yi korafi akan neman gwamnati ta kara mata kudade ba”

Wannan ya biyo bayan yadda ‘yan Najeriya ke faman kace-nace a game da yadda hukumar ta dage zaben.

Daga Na’Allah Raheemeeb

HANYAR JIRGI DABAN TA MOTA DABAN

Idan har jita jitar da ake yadawa cewa wasu suna kokarin yaudarar mutanen malam Ibrahim shekarau a karamar hukumar Kumbotso su zabi Ballah a majalisar tarraya hakane da gaske akwai to tambayar ita ce su wanene kuma mutanen ballah ne ko mutanen sardauna ne ?

Ba mutanen sardauna bane !

Watakil idan akwai maganar da gaske to mutanen kwankwasiyya ne suka kirkirota dumin kawo kokwanto ga raunan mutanen sardauna

Amma abin lura shine meyasa Ballah yake yawo da Ali Madaki a matsayin Dan takarar sa na sanata Wanda nasan mutane da yawa sun ganshi a sheka ,shagari Quarters jao’ji gidan zoo da sauran gurare a Kumbotso yana tallata Dan takarar sanatan PDP

Kirana gare mu shine jam’iyyar APC zamu zaba a wannan zabuka masu zuwa mu kaucewa yan fasa fasa musha ruwan kwai

Allah ya bamu nasara amin

1 Muhammad Buhari

2 Maigirma Sardauna

3 Munniru Babba

Daga Sulaiman Ibrahim Kura

Zirga-Zirgar Jiragen Sama

#S4S2019

Domin saukaka zirga-zirga a filayen sauka da tashi na jiragen sama musamman wajen tura kayayyakin zabe zuwa ga Jahohin Kasar Najeriya a zaben da za’a gudanar, hukumar zirga-zirga ta jiragen sama wato NAMA ta sha alwashin barin sararin samaniya a bude kafin zabe da lokacin zaben da kuma bayan kammala zaben inji Babban Manajan Hulda da Jama’a Kahalid Emele.

Wannan ya biyo bayan umarnin da Karamin Ministan kula da yanayin sararin samaniya a Najeriya Sanata Hadi Sirika ya bayar na ci gaba da zirga-rirga awa ashirin da hudu (24hrs) a duk filayen sauka da tashi da ke wannan Kasar ta Najeriya.

Daga Na’Allah Raheemeeb

Jami’an Tsaro A Kano

JINJINA GA JAMIAN TSARO NA JAHAR KANO.

Tabbas cikin kwana biyun nan mu al’ummar wailari da maikalwa muna farin ciki da zagayen da jamiaan tsaro sukeyi a wannan yankuna namu domin tabbatar da tsaro wanda a baya yake ta addabar mu, mai girma commissioner of police allah ya saka da alkhairi, allah ya kara mana zaman lafiya.

Comr Yasir Sani Tahir
17/02/2019

ILLOLIN DA KWANKWASO YAYIWA KANAWA

1. Durkusar da Walwalar ‘Yan fansho
Kwankwaso yagaji asusun ‘Yan Fansho makare da biliyoyin nairori, kafin zuwan sa dazarar Ma’aikaci yayi Murabus cikin kankanin lokaci yake samun Hakkinsa, amma lokaci daya ya kwashe kudaden yamaida su kudin Kwankwasiyya, eh mana! Ai kauyen Kwankwasiyya yagina dasu, yakuma rabawa wasu Kwankwasawan kyauta, yau ma’aikaci in yayi retire hakkin sa sai mama tagani.

2. KOYAWA MATASA RASHIN KUNYA
Salon sa na cin mutuncin manya wadanda yake ganin barazana ne ga son zuciyar sa yasa wasu daga Matasan Kano sun dauka keta mutunci shine siyasa, yau matasa kan rufe Ido suci zarafin sa’annin Iyayen koma Kakannin su da sunan hamayyar siyasa.

3. FARFADO DA SIYASAR SARA SUKA
Tun sanda akayi zaben cike gurbi na Gaya da Garko tsakanin ANPP da PDP siyasar sara suka ta farfado, kuma Gwamnatin Kwankwaso ce ta dauki nauyin ‘Yan Sara suka ta sanya su Abdullahi Abbas suka Jagorance su wajen mamaye tashoshin zabe da makaman su, suka hana duk wani wanda kansa babu Jar hula kada kuri’a, hatta Sanata Kabiru Gaya sai dawowa yayi gida batare da jefa kuri’ar sa ba.

Wadannan kadanne daga illolin, Muhadu a rubutu nagaba.

#SayNoToKwankwasiyyaIdeology

Daga Umar Faruq Muhammad

Katobarar ‘Yan Siyasa

Allah da kansa a cikin littafinsa mai tsarki yace Yaku Wanda kukayi Imani Kuji tsoron Allah Yaku Wanda kukai Imani kukiyaye kanku da iyalanku daga wuta Yaku Wanda kukai Imani kutuba daga laifikanku tuba Na har abada Sannan Annabi Muhammad (S.A.W) Yaqara cewa akwai wata tsoka ajikin mutum inta gyaru gangar jiki yagyaru intabaci to ya baci yaqara mana da mukiyaye harshenmu kar yakaimu ga shiga wuta Allah ya karemu sannan yaqara da in zakayi magana ka Fadi Alkahiri ko kayi shuru Ya YAN uwana ina hankalinmu da tinaninmu yake har za mudinga fade-fade marasa kyau ga malamanmu Na addini Dan sun samu sabani da YAN siyasa toh wlh duk abun da muka rubuta ko mukafada zamu bada hujja Agaban Allah.Allah yasa mugane Gaskiya Mu gyara Ameen. Ansamu Dan siyasa Wanda ba musulmiba yayiwa fatiha yadda yaga dama a sokoto ansamu Yar siyasa tayiwa alam nashrah yadda ta ga dama a Abuja ansamu Wanda yace baruwansa da malintarka ko shekara dubu zakayi amasallaci iyakaci yazo kaja Sallah ya fita yabarka a masallacinka a kano gawani yace ko Allah da kansa zai irga quri’ah Buhari yafadi kaji irin mutanen da suke so su jagorancemu

Daga Sadik Haladu Gama

YAUDARAR KWANKWASIYYA

Idan Mutanen Kano basu manta ba a kakar zaben 2011 lokacin dawo-dawon Kwankwasiyya sun rabawa Matan jihar Kano Fama-famai tare dayi musu alkawarin bayan zabe zasu basu jarin dubu Hamsin-Hamsin.

Bayan an kammala zabe sunyi Nasara mata suka ji shiru ba’a waiwaye su kan batun Jarin ba, hakan yasa suka aika tambaya a gidajen rediyo don sanin inda aka kwana.

In baku manta ba saboda rashin Kunya sai Gwamnatin ta aika Ali Baba Agama lafiya yabada amsar cewa wai abokan Hamayya ne suka raba forms din don su hada Gwamnatin da rigima.

Duk wanda ke bibiyar siyasar Kano yasan anyi haka.

Wannan form din dake kasan rubutun nan dazu nakarbe shi anbawa wata cousin sister ta, kuma wanda yabata Dan Kwankwasiyya ne, ina gani sai labarin dana rubuta asama yafado min, nace wato Damfarar Kwankwaso ta 2011 irinta suka kullawa Abba?

To kusani fa kan mage ya waye, sai dai ku damfari gidadawa.

Daga Umar Faruq Muhammad

Hukumar Zabe A Najeriya Ta Nemi Afuwa

#S4S2019

Hukumar zabe a Najeriya ta nemi afuwar yan Kasar sakamakon dage zabe da tayi ‘yan awoyi kadan kafin a gudanar da zaben ranar Asabar 16/2/2019

Dagewar ta jawo kace-nace a tsakankanin Jam’iyyar dake kan mulki ta APC da kuma Jam’iyyar adawa ta PDP a hannu guda kuma ta jawo asarar dukiya mai dinbin yawa

Hukumar zaben ta sake sa wata sabuwar ranar gudanar da zaben ranar Asabar 23/2/2019 da kuma 9/3/2019. Inda hukumar tace sun sami matsala ne a bakwai (7) daga Jahohin Kasar talatin da shida (36)

Abin tambaya anan shine, yadda aka rarraba kayan zabe a sauran Jahohin kuma dayawa daga muhimman kayan zaben da suka zama na sirri ne sun riga sun shiga hannun mutane, menene abin da hukumar zatayi na hana yin magudi sakamakon hakan?

Daga Na’Allah Raheemeeb

Daga Ofishin Yakin Neman Zaben Shugaba Buhari

#S4S2019

Ofishin yaki neman zaben shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi allawadai da matakin hukumar zaben kasar, INEC, na dage manyan zabuka.

Hukumar zaben ta ce ta dage zaben shugaban kasa daga ranar 16 ga watan Fabrairu zuwa 23 ga watan na Fabrairu.

Kazalika za a gudanar da zaben gwamnoni ranar tara ga watan Maris maimakon ranar biyu ga watan na Maris.

Daga Na’Allah Raheemeeb

Hukumar Zabe A Najereriya Ta Dage Zaben Shugaban Kasa Da Majalisar Dattijai Da Ta Tarayya

#S4S2019

Bayan zaman da hukumar zaben tayi a daren Jumma’a 15/2/2019 ta dauki kudirin dage zaben da ta shirya gudanarwa na Shugaban Kasa, Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai ta Kasa a ranar Asabar 16/2/2019 zuwa ranar Asabar 23/2/2019.

Haka kuma za’a gudanar da zaben Gwamnoni da Majalisar jahohi ranar Asabar 9/3/2019

Wannan ya faru sakamakon rashin kammaluwar wasu muhimman ayyuka da hukumar ta ce bazai bada damar gudanar da zaben ba, ita kuma tana so ta gudanar da sahihi kuma karbabben zabe a duk Kasar

Daga Na’Allah Raheemeeb

Mu Zabi Mallam Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano

Ina rokon ku dan girman Allah dan kadaitar zatin sa idan Allah ya kaimu gobe ku fito ku dangwalawa maigirma sardaunan kano kuri’a

Duk wanda muka bata masa a baya ko a rashin sani ko da sanin mu yayi hakuri ya duba matsayin kano central ya zaba mata mutum managarci kamili

Ina neman alfarmar dukkan abokai na da wadanda suke siyasa da wanda basa siyasa da kuma na sauran jam’iyyu su daure su zabi cancanta wato malam ibrahim shekarau

Allah ya bamu nasara da rinjaye (amin)

Daga Sani Adamu Hotoro

‘Yar Manuniya Ta Nuna

Tun daga sauna zuwa dakata zuwa zango zuwa rimin kebe zuwa gayawa zuwa fanisau zuwa jaba zuwa sabon birni zuwa rafin malam zuwa titin danrimi zuwa rijiyar lemo zuwa kurna zuwa gobirawa dandazon mutane ne wasu a kasa wasu a kekuna wasu a mashina wasu a motoci wasu kuma sunyi dandazo a gefen tituna suna murna da ganin maigirma gwamna da Sardaunan Kano Gaskiya a yau naga dan adam mutane sun nuna mana kauna, fatan Allah ya bamu nasara a wannan zaben da za’a gabatar na ranar asabar 16/2/2019

Sani Adamu Hotoro secretary general
#S4S_Nassarawa

Rama Alkhairi Da Alkhairi

Nayi karatu kyauta a Government Girls secondary school yar’gaya har Sardaunan kano yasauka daga mulki Dan zanyi APC ranar Asabar Insha Allahu
Zan Rama Alkairi da Alkairi

Daga Humaira Salisu

#Shekarau4sanate

Buhari, Ganduje Sardauna

#S4S2019

H.E Mallam Ibrahim Shekarau CON (Sardaunan Kano) ya tabbatarwa duniya cewa, “a iya sanina bani da wani sabani da Shugaba Buhari.

Illa dai kawai akwai wasu mabiya wadanda suke kirkirar sabani a tsakanin mu domin samun biyan bukatar kansu.

Kuma Insha Allah zamuyi aiki tare da Shugaba Buhari yayin da muka haye kujerun mulki.” Inji Sardaunan Kano

Daga Na’Allah Raheemeeb

Nagartaccen Mutum

Ubangiji ga bawan ka nagartacce wanda baya cin mutuncin kowa saboda biyan bukatar kan sa wato Sardaunan Kano ka dora shi akan dukkan abokan hamayyar sa ka bashi rinjaye da nasara a kan su

Sani Adamu Hotoro secretary general
#S4S_Nassarawa

Kada Ku Jefa Jahar Kano Cikin Fitintinu – Sarki Muhammadu Sunusi II

#S4S2019

Mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sunusi II ya yi gargadi ga jagororin siyasar Jahar Kano da ma yaransu da kada su kuskura su jefa Jahar cikin fitintinu da rudanin siyasa kawai saboda neman bukatunsu na siyasa

Sarkin yace ya zama dole ya yi wannan kira ga jagoroin siyasa, duba da yadda suke tunzura matasa suna cin mutuncin mutanen da basu ji basu gani ba, inda suke bin wasu har gaban iyalansu.

“Mun yanke shawarar ganawa da manema labaru ne bisan rahotannin da muka samu dake nuna akwai babbar barazana ga rayuwar jama’an Kano da dukiyoyinsu. Muna kira da a zauna lafiya tsakanin yan siyasa da jama’an gari.

Siyasa fa ba yaki bane, idan har kana da katin zabe, sai ka zabi duk wanda ya kwanta maka rai ya zama shugabanka.” – Mai martaba Sarki

Sarkin ya yi kira ga yan siyasa dasu kiyayi jaye jayen mutanen da basu sansu ba, domin kada su aikata munanan ayyuka da sunansu, don haka yayi kira ga hukumomin tsaro dasu tashi tsaye wajen gudanar da aikinsu tare da kama duk wasu miyagun mutane.

Sarkin ya yi kira ga hakiman sa dasu tabbata sun bada goyon baya da hadin kai ga hukumomin tsaro ta hanyar mika duk wasu wadanda suka aikata laifi ga hukumar Yansanda ba tare da bata lokaci ba.

Yayi addu’ar Allah yasa a gudanar da zaben 2019 cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali, tare da yin kira ga jama’a dasu kasance masu bin doka da oda a Jahar Kano da ma kasar gaba daya.

Daga Na’Allah Raheemeeb

Idan Kunne Ya Ji…

#S4S2019

Al’ummar Kano da ma na sauran Jihohin Najeriya kuyi nazari da duba na tsanaki akan wadanda zaku basu amanar kanku da dukiyoyinku da mutuncinku da addininku. Wadannan sune masu girmamaku su girmama malamanku da dattijanku da shugabanninku.

raba kanku da masu kokarin cin zarafinku da dukiyoyinku da mutuncinku da addininku. Ta haka ne kawai za ku kauracewa wawayen cikin ku da gidadawan cikin ku da shedanun cikin ku da jahilan cikin ku harma da yaransu da abokanansu da yan koransu da masu goya musu baya.

Daga Na’Allah Raheemeeb

SANARWA TA MUSAMMAN

Akwai hira Da za’a gabatar da dan takarar Sanatan kano ta Tsakiya Mal Ibrahim Shekarau a gidajen Radio kamar haka:-

Daga gobe Talata.

12/02/19 Talata

Rahma Radio 9:00-10:00 pm na dare
Radio Kano 9:00-10:00 pm na dare
Dala Radio 11:00 – 12:00 pm na dare
Arewa Radio 11:00-12:00 pm na dare
Pyramid Radio 11:00-12:00 pm na dare
Express Radio 11: 00-12:00pm na dare
Freedom Radio 11:30-12:30 na dare

Laraba 13/02/19

Aminchi Radio 8:00-11:00 na dare
Pyramid Radio 10:00-12:00 na dare
Dala FM 11:00-12:00 na dare

Alhamis 14/02/19

Guarantty Radio 6:30-8:30 na yamma

Ismail Lamido
Mai lura da yanar gizo na
Mal Ibrahim Shekarau

WAJIBI DUK MAI KISHIN ADDININ SHI YA KAURACEWA RABI’U KWANKWASO HAR SAI YA BAYYANA TUBA

Daga Mallam Anas Assalafiy Fagge
WAJIBI DUK MAI KISHIN ADDININ SHI YA KAURACEWA RABI’U KWANKWASO HAR SAI YA BAYYANA TUBA

Ga duk mai bibiyar maganganun Rabi’u kwankwaso ya san cewa duk lokacin da ya samu gabar da zai iya amfani da ita wajen sukan wata alama ta addini Ko masu addini to Sai yayi hakan gaba-gadi !

Kwankwaso ya Jima yana cin mutuncin GEMU da DAGE-WANDO ! Duk da cewa Annabi Alaihis-salam ne yayi umarni Da su.
Annabi Alaihis-salam Yana cewa:
أحفوا الشوارب، ووفروا اللحى؛ خالفوا المشركين
Ma’ana:
“Ku rage gashin baki, Ku cika gemu, Ku sabawa mushrikai”
(Bukhari da Muslim suka rawaito daga Abdullahi dan Umar Allah ya Kara musu yarda)
A ruwayar Nasa’iy kuma daga Zaid dan Arqam Annabi Alaihis-salam cewa yayi
” Ku rage gashin baki,Ku cika gemu, Ku sabawa majusawa”

Haka nan Annabi Alaihis-salam bai bar batun dangale TUFAFI ba Sai Da yace:
ثَلَاثَةٌ لَا يُكَلِّمُهُمُ اللهُ يَوْمَ الْقِيَامَةِ، وَلَا يَنْظُرُ إِلَيْهِمْ وَلَا يُزَكِّيهِمْ وَلَهُمْ عَذَابٌ أَلِيمٌ:الْمُسْبِلُ، وَالْمَنَّانُ، وَالْمُنَفِّقُ سِلْعَتَهُ بِالْحَلِفِ الْكَاذِبِ
Ma’ana:
“Mutane uku Allah ba zaiyi magana dasu ba ranar alkiyama, ba zai kalle su ba ( duba na Rahma), ba zai tsarkake su ba (daga azaba) kuma suna Da azaba mai radadi, sune:
MAI BARIN TUFAFIN SHI YA WUCE IDON SAHU, MAI YIN GORI DA MAI YIN RANTSUWAR KARYA A WAJEN CINIKI”
( Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta 106).

Amma duk da wadannan dalilai kwankwaso burinshi ya soki wadannan halayyar Da Annabi Alaihis-salam yazo mana da ita, bayan kuwa Allah umartar mu yayi Da rike abinda Annabi yazo dashi, duba suratul hashri Aya ta 7.

Masu irin wannan halin na kwankwaso idan Basu tuba ba suna ridda su fice daga addini ba tare da sun Sani ba !

Allah Yana fada a cikin suratul-Tauba Aya ta 65-66 cewa:
وَلَئِن سَأَلْتَهُمْ لَيَقُولُنَّ إِنَّمَا كُنَّا نَخُوضُ وَنَلْعَبُ ۚ قُلْ أَبِاللَّهِ وَآيَاتِهِ وَرَسُولِهِ كُنتُمْ تَسْتَهْزِئُونَ (65) لَا تَعْتَذِرُوا قَدْ كَفَرْتُم بَعْدَ إِيمَانِكُمْ ۚ إِن نَّعْفُ عَن طَائِفَةٍ مِّنكُمْ نُعَذ

Fagge, Nassarawa, Tarauni

Mai Girma Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje OFR da tawagar sa sun halarci gagarumin taron yakin neman zaben jamiyar APC na kananan hukomomin Tarauni, Fagge da Nasarawa wanda akayi a Kaura Goje dake karamar hukumar Nasarawa.

hukumar ta Nasarawa itace mafi yawan kuri”u a duk Nigeria da kimanin kuri’a dubu dari hudu da uku, 403,000. Haka zalika karamar hukumar ta Nasarawa itace karamar hukumar Mataimakin Gwamna Dr Nasiru Yusuf Gawuna, da tsohon Gwamna kuma dan takarar Sanatan Kano ta tsakiya Mallam Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano, dan haka muma sa ran ita kadai zata bawa Gwamna Ganduje kuru’un da zasu sa ya linka sauran abokan hamaiyar sa.

irin gangamin da yan kananan hukukomin nan guda uku sukayi a yau, wannan tabbacin nasarrar lashe zaben Gwamna Ganduje ne da sauran yan takarar Jam’iyar mu ta APC a jihar Kano.

karshe Gwamna ya karbi yan Kwankwasiyya da suka chanza sheka a karamar hukumar Nasarawa bisa jagorancin Abba Boss, da kuma Sarkin Hawan Kara na Kano da sauran su.

Sai Baba Uban Abba.

Daga Ibrahim Z Bello Kura

Yau 11/2/2019 Karfe 9:00 Na Dare

#S4S2019

A saurari hira ta musamman da Maigirma Mallam Ibrahim Shekarau CON (Sardaunan Kano)

Gidajen radion Express, Guarantee da Aminci.

LALACEWAR ZAMANI CE TASA IRE-IREN KA SUKE MULKAR MU

A cikin abin takaicin dana saurara a jawabin tsagerancin da Sanata Kwankwaso yayiwa Mallaman Addini naji ya gargade su cewa su tsame bakin su daga shiga harkar Siyasa, sukyale su sune ‘Yan Siyasa suyi abarsu, in bahaka ba shima yanada Mumbarin sa zai ringa amfani dashi yaci zarafin su.

Akan haka nake so inja hankalin Kwankwaso da masu rabe Addini da Siyasa su sani cewa tunanin su gajeren tunani ne, hakanan kuma Makafin Idanu ne dasu shiyasa suka kasa sanin cewa “AL ISLAMU DININ SHAMIL”.

Muslinci Addini ne dazaka iya kiran shi Komai da ruwanka, duk wata sabga data shafi Addini da rayuwa to Muslinci da Musulmai sunada ruwa da tsaki acikin ta.

Dayake mu akasar Hausa muke bari in tunawa Kwankwaso da masu irin tunanin sa DAULAR USMANIYYA ta Sheikh Usmanu Dan Fodio, shin su Kwankwaso basu taso sun tarar da Masallatai a gidajen Sarakuna da Hakimai ba a garuruwan da Daular Dan Fodio ta mulka?

Hikimar da tasa muka taso mukaga haka shine, Sarki shine Shugaba, shine Limami, shine Fitilar Al’umar dayake mulka a fannin addini da lamuran rayuwa.

Turawa ‘Yan kama wuri zauna sune sukazo suka rusa wancen tsari saboda gabar su da Addinin Allah, a irin Illar dasuka yi mana ne suka karbe ragamar Shugabanci daga Mallamai suka mikata ga ‘Yan Bokon dasuka kyankyasa marasa Addini.

Wannan illar ce ta maida mulkin mu wajen ire-iren ka, kuma nauyi ne akan duk Mai kishin Addini yayi fafutukar dawo da shugabanci hannun wadanda suka tarbiyantu da Ilimin Addini.

Daga Umar Faruq Muhammad

Design a site like this with WordPress.com
Get started