
INNAH LILLAHI WAINNAH ILLAIHIR RAJUUN!
NACIKA DA MAMAKI AKAN ABINDA MALAM IBRAHIM SHEKARAU YAYI.
Cikin wani yanayi naban mamaki tareda alhini Wanda masu iya karatun turanci da rubuntun turanci kan Kira (surprised) ko (marvellous)
Haduwarmu keda wuya yayin isarda sakon da megidana ya turani jahar jigawa dutse, a tashar mota a yau,
Sainaji ance salam alaikum, na amsa da waalaikassalam, dan Allah Abokina ko kaine Nura sani jibrin Gwagwarwa, Sardaunan matasan Gwagwarwa,? Nace kusan hakanne Amma meyasa kake tambaya Nura Sani Jibrin Gwagwarwa ko yayi maka laifi ne?
Sam ko kusa kawai ina kaunarsa kamar yadda yake kaunar Sardaunan Kano, kuma na dogara da shafukansa wajen sanin dukkan ababan daya shafi harkar siyar Gidan Sardaunan Kano dama jahar Kano baki daya kasan yanda yake tiri tiri da kare dukkan wani abu da zaimanto ya danganci Sardaunan Kano,
Nace hakane? Yace eh wallahi dan haka nake son Zama aminin sa ta kowace hanya.
Rufe bakinsa keda wuya Sai wata Baiwar Allah tace Kamar kuna maganar Mal Ibarahim shekarau?
Nace hakane hirar sa mukeyi.
GYARA ZAMA KUSHA LABARI.
Acewar wan nan baiwar Allah ashekara ta 2006 tashiga cikin masifa da Balai irin Wanda bata taba ganin irinsaba, Amma sakamakon Mal Ibrahim shekarau ta fita ta numfasa saita fashe da kuka tareda adduoi kamar haka,
Allah yanda Mal Ibrahim shekarau yashare Mana hawaye kashare Masa nasa Nace Amin.
Allah ka suturtashi kamar yanda ya suturtamu Nace Amin
Tace ubangiji ina tawwsali da dukkan wani aiki danayi ka karba daka biya dukkan wani Abu da Mal Ibrahim shekarau zainema a gurinka ka biya Masa Nace Amin.
Allah karabashi da duniya lafiya shida dukkan makusancin shi Nace Amin.
Uhmn! Tacigaba kamar haka, a wan nan shekarar Munkasance a gidan gadon mijina wanda su biyu sukayi tarayyah akai,
Bayan tsawon shekaru mun hayay yafa harshi megidana takaiga karfisa yayi kasa kwatsam sai dan uwansa dasuke ciki daya yakaishi kotu domin araba gado kokuma ayi sulhun gado musaya afiddashi,
Abu kamar wasa akai cinikin gurin Naira Miliyan daya da dubu dari bakawai, mukayi alqawarin biyan kudin Amma Kash Allah bai hore manaba,
Ga Yara har Guda Tara gashi Abinda zamuci shikansa kullum sai a hankali domin dreba ne megidana a lokacin Babu mota han nunshi.
Na rasa Abinda yake min Dadi kawai saina yanke shawara Koda zan mutu zanje gidan Gwamnati bakuma zandawoba Koda kwana nawa zanyi tunda naji yanda Gwamna yake taimakawa alumma Ina sa ran wataqil in an isar da sakon mu ya iya biya mana koda kudin hayane mu koma kafin asaida gidan.
Zuwana gidan Gwamnati keda wuya Sai maaikatan tsaro suka hanani shiga Tareda kiranada mahaukaciya magan ganu kala kala kin dauka Gwamna kamar kene duk lokacin da ake so zaa Ganshi? Wasu masu hankali naban shawara inje radio anacikn haka saiga wani Bawan Allah yafito daga cikin gidan Gwamnati a motarsa zaifita.
Sai shi wan nan mutum ya tsaya dukkan ma aikatan suka juya da kiransa ranka yadade wani kusadani Naji yace S.A. dayan Kuma yace Yarima ne.
Bayan ya saurari dukkan abinda ke tafe dani yana Shirin fara yimin magana sai wayarsa irin Mai Budewar nan tayi Rin sainaji yana cewa ok sir yes sir ina gate, sai yacemin toke bari an kirani Amma kijirani tukun muga ta Ina zamu bullowa lamarin, yabawa jamian tsaron ummarni da su bani guri in jira shi.
Bayan yashga kamar da Minti 30 sainaga yafito tareda tambaya a Ina gidan yake Kuma inshirya mutafi Allah yadubi zuciyata,
Kiran da akaimasa Maigirma Gwamna ne yakirashi domin bashi wasu ayyuka, shine yake tambayarsa dama baka fitaba kenan? Nace Masa nazo fita amma ga Abinda ya dakatar Dani, yanaji haka sai shi Gwamna yace nawa ne kudin gida nagaya Masa Miliyan daya da dubu dari bakawai, Abin mamaki sai yace Ina zuwa yashiga cikin dakinsa ya dauko Naira Miliyan Biyu Tareda umartata da muje asiyi Gidan in dam ka miki takardun gidan Kuma in baku ragowar dubu dari uku kuyi gyare gyare da siyan kayan Abinci kuyi zaman ku.
Hakan Kuma akayi, mukaje yasamana gidan a ranar akabamu takar dunmu aka Kuma bamu ragowar kudin shikansa wallahi ko Naira bai cire ba haka ya wanzar da abinda aka Dora Masa.
Dan haka Nida yayana da megidana baza mudaina yima Sardaunan Kano Kuma sanatan Gobe danizinin Allah Mal Ibrahim shekarau adduaba har iya karshen rayuwar mu inshallah.

Hakan yasa matsayina na Masoyinsa Mai kaunarsa duda Ana kokarin rabamu dashi na gabyadace in bada lokacina tunanina fahimtata in Kara fitoda kyawawan halayen sa,
Hakika Ina alfaharin da samun jagora Abin sawa agaba ayi tun kaho dashi Sardaunan Kano Mal Ibrahim shekarau.
Daga
Nura sani jibrin Gwagwarwa
Sardaunan matasan Gwagwarwa.
Masoyin Sardaunan Kano idan har baa Rabamuba.
Kuhuta lafiya.
You must be logged in to post a comment.