Ibrahim Z Bello Kura

SHUGABA BUHARI ZAI KAFA TARIHI

Hukumar kula da albarkatun man fetur na ‘kasa (NNPC) ta fitar da sanarwan cewa gobe asabar 2-2-2019 shugaba Muhammadu Buhari zai kaddamar da sabbin rijiyoyin men fetur da aka samu nasaran tonawa a yankin kogin Kolmani dake karamar hukumar Alkaleri jihar Bauchi

Wannan shine karon farko a tarihin duniya da akayi nasaran tona rijiyoyin man fetur a arewa kuma a karkashin gwamnatin shugaban ‘kasa Muhammadu Buhari, sannan jihar Bauchi zata shiga jerin jihohi masu arzikin man fetur a Nigeria

Wannan nasarane daga Allah, Baba Buhari mungode.
Allah Ka taimaki shugaba Buhari Ka kara masa taimako da nasara Amin

Ismail Muhammad

ZUWAN SHUGABA BUHARI KANO,YA JEFI TSUNTSU UKU DA DUTSE DAYA:

Ziyarar yakin neman zabe da kaddamar da ayyukan raya kasa da Mai girma Gwamnan Kano,Dr Abdullah Umar Ganduje ya gabatarwa Kanawa.Ziyara ce da ta dauki hankali da sa ido har ma da kunnuwa na masu bibiyar harkokin siyasar Kano,da ma ta shi kansa Shugaba Muhammadu Buhari.

Dalili na farko shi ne,irin farfagandar da masu hamayya da Gwamna Ganduje da jam’iyyar APC a Kano,musamman ma yan darikar Kwankwasiyya ke yadawa,kan tsamin da suke cewa wait dangantaka ta yi tsakanin Shugaba Buhari da Gwamna Ganduje.Kan maganar fefen bidiyon dala,mai kama da wasan kwaikwayo.Ta yadda suke cewa,Buharin ba zai zo Kano ba,saboda manufarsa ta yaki da cin hanci da rashawa.

Dalili na biyu kuma shi ne,su dai ahalin Kwankwasiyya na yada farfagandar cewa,saboda wai ba bu dangantaka mai kyau tsakanin Mai girma Sardaunan Kano Mallam Dr Ibrahim Shekarau da Shugaba Buhari,kuma ganin yadda Gwamna Ganduje,ya yi ruwa,ya yi tsaki gurin tabbatuwar dawowar Sardauna zuwa APC,da ma ba shi damar yin takarar Sanatan Kano ta tsakiya kai tsaye a jam’iyyar.Wai wannan ta sa Buharin ya kullaci Ganduje,kuma ya sha alwashin ba zai zo Kano don daga hannunsa ba lokacin yakin neman zabe.

Dalili na uku kuma da su dai yan hamayyar ke fada da zai iya hana Shugaba Buhari zuwa Kano shi ne,saboda wadancan dalilan biyu na sama,Shugaban ya fi amincewa da takarar wani dan takara na wata jam’iyyar adawa a Kano,hasalima shi zai baiwa magoya bayansa umarnin su zaba a Kano lokacin zabe.

Saboda haka kurun kus,ga shi dai Shugaba Buhari ya zo Kano.Na farko, ya kuma daga hannun Gwamna Ganduje,a matsayin dan takarar Gwamna jam’iyyar APC a Kano.Harma ya kaddamar da ayyukan raya kasa na mai girma Gwanan.Na biyu,ya yi musabiha da Sardaunan Kano Mallam Dr Ibrahim Shekarau a gaban milyoyin al’umar Kano.Na uku kuma ya yi alamar 4+4 da ta fi shahara a Kano gurin bayyana bukatar Gwamna Ganduje na sake maimaita mulkin Kano karo na biyu.Ya na kuma fadin “da yardar Allah za mu kara” ma’ana shi da mai girma Gwamna Ganduje,za su kara 4 a kan wata 4 a mulki.Ba bu kuma inda ko da wasa ya ambaci sunan wani dan takara na wata jam’iyya a matsayin wanda ya ke marawa baya.Ko dai dai da yin shagube.

Da wadan nan dalilai,tabbas Shugaba Buhari,ya jefi tsuntsaye uku da dutse daya a lokaci guda,kuma tabbas ya yi nasrar samunsu a makasa.Manyan wadanda suka ci nasara a wannan ziyara ta Shugaba Buhari zuwa Kano su ne,na farko Mai girma Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje.Na biyu Sardaunan Kano Mallam Dr Ibrahim Shekarau.Ta uku ita ce jam’iyyar APC reshen jihar Kano,karkashin jagorancin Dan Sarki,Alhaji Abdullahi Abbas.Saboda Nagoya bayanta sun sami Karin karsashi da kuzarin tukarar yan hamayya a zabe mai zuwa.Sai kuma milyoyin al’umar Kano dake kishirwar ganin Shugaba Buhari,wadanda suka fito,fita irin ta dango suka yi ido hudu da shi.

Fatanmu shi ne,Allah Ya sa a yi zabe lafiya,a gama lafiya.Jam’iyyar APC ta ci nasarar lashewa daga sama har kasa,a jihar Kano da fadin Nigeria.

Bangajiya

#S4S2019

Sakon bangajiya ga dubban daruruwan masoya, magoya baya da masu fatan alkhairi ga H.E Mallam Ibrahim Shekarau CON (Sardaunan Kano) wadanda suka sadaukar da ayyukansu, kasuwancinsu da dukkanin hidindimunsu suka fito tun da sanyin safiya domin yi masa rakiya wajen taren Shugaban Kasa Buhari a ziyarar yakin neman zabe daya kawo Kano ranar Alhamis 31/01/2019
Muna godiya Allah ya kaimu ranar rantsuwa, tare da fatan kowa ya koma gida lafiya

Daga Na’Allah Raheemeeb

Abba A Abdullahi

Wannan daga hannun nafi tinanin editing ne! Dan yan kwankwasiyya sunyi rantsuwa baba ba zai daga hannun sa ba.

Rantsuwa uku da yan kwankwasiyya sukayi akan ganduje da buhari kuma yau Buhari duk ya karya su

1- buhari ba zaizo
2- in yanzo kano bazai shiga gidan gwamnati ba
3- in yazo kano ba zai daga hannun ganduje ba

Ku kuwa me yayi zafi haka yan Uwa! 😂

Bari na fece kafin su zo🏃🏃

Bada Tuta Ga ‘Yan Takara

Shugaban Jam’iyya Ya Mika Tuta Ga ‘Yan Takara

Kamar yadda wani gidan radio a Jihar Kano ya bada rahoto cewa, an mikawa ‘yan takarkarun APC tuta a filin wasa na Sani Abacha, amma ba shugaba Buhari ne ya mika tutar a garesu ba.

Wannan gidan radio ya kara da cewa, Buhari bai ce SAK ba kamar yadda ya saba fada a sauran jihohi, sai kawai naji maganar kamar wani yarfe na siyasa, kuma nayi takaici, kasancewar gidan radio fitacce wanda ke da ‘yan jaridu fitattau hade da fitattun masu tace labarai ke yada wannan labaran

Ina so na tunasar da wannan gidan radio cewa, bada tuta ga duk wani dan takara tun daga kan shugaban Kasa har kansila aikin Jam’iyya ne, wanda Shugaban Jam’iyya ke da alhakin gabatarwa kokuma duk wanda shugaban Jam’iyyar ya wakilta.

Sai kuma furta Kalmar SAK, wanda yake nufin ayi zabe tun daga sama har kasa, amma dai tunda Buhari ya daga hannun Gwamna amma dai yace ranar zabe mu fita muyi zabe cikin mutunci zamuyi nasara kuma zamu kara, ai magana ta kare.

Daga Na’Allah Raheemeeb

#S4S2019

Kurunkus

Ranar Kanawan Dabo

Mai Girma Gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje OFR da mataimakin sa Dr Nasiru Yusuf Gawuna da tsohon mataimakin sa Farfesa Hafiz Abubakar da tsohon mataimakin Gwamna Abdullahi T. Gwarzo da

Minista Abdurrahman Dambazau da Gwamnonin Zinder da Maradi daga jamhuriyar Nijar, sauran manyan Jami’an gwamnatin jiha da na taraiya sun shirya domin zuwa filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano domin taro Shugaban Kasa Muhammad Buhari wanda zai zo kaddamar da yakin neman zaben sa a Jihar Kano a yau.

Salihu Tanko Yakasai
Special Adviser Media
Government House Kano
January 31, 2019

Mazabata abin alfahari na

Mu hadu a akwatun zabe

Ni in sha Allah Daga yanzu na koma da komai nawa zuwa mazabata. Domin itace mutunci na A siyasa. Duk cika bakin Dan siyasa da Dagawa, da Shige shigensa bashi da mutunci In har bai ci mazabarsa ba, da Akwatunsa ba. In sha Allah kamar yadda nasaba cinye akwatuna da mazabata wannan karan ma haka zanyi. Basu tunanin wani abu akan mu, ko dan mun fadi gaskiya agyara wasu sunce Hassada ake, wasu sunce Tura kai muke. To magana ta Kare Allah ya kai mu zabe. Kowa zamuga masu ado da kwamati ko iya sa riga da sitati. Dan haka mu hadu bayan zabe.
#MIKIYA.
MAZABATA ITACE MUTUNCINA.
AKWATUNA SHI NE TAKAMATA.
NASARAR SARDAUNA ITACE ALFAHARI NA.
KU MUHADU A FILIN ALLAH TSINE UWAR MAI KARYA MA’ANA COLLECTION CENTER. TA KANANA HUKUMOMIN MU.
IDAN NAI KUSKIRE A RUBUTUNA A GYARAMUN DAN NI KAM BA A’HAIFIN DA IYAWA BA . KUMA BANA SAWA AYIMUN RUBUTU DA HARSHAN NASARA NAI POST DINSA A ZUWAN NI NAI.
KUNSAN MALLAMAI MA SUNCE BAN SANI BA ITAMA RABIN ILIMICE.

Sanatan Kano Ta Tsakiya

#S4S2019

Gwabnatin Mallam Ibrahim Shekarau tafi kowacce irin gwabnati daukar ma’aikata a tarihin Jihar Kano. Muna kyautata masa zaton zaifi ko wanne sanata samowa ‘yan Kano federal appointments. Allah Ya shiga cikin al’amuransa Ya bashi sanata.

Zaman Kwamitin Social Media Na Farko

OPERATION ANKAWO KARSHEN KORAFI.

sanarwa ta mussamman daga DG Social Media JAGORA Mal Bello Muhammad Sharada ga duk wanda baiji sunansa ba yayi COMMENT domin shiga cikin kwamitin koli yakin neman zaben Dr Ibrahim Shekarau a Social Media

Kaddamar Da Kwamitocin Yakin Neman Zabe

Laraba

30/01/2019
Mai Girma Dantakarar Sanatan Kano ta Tsakiya Dr Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano Ya kaddamar da Kwamatocin Takararsa .
Mai bawa Sardaunan Kano Shawara a harkar Siyasa
Alh Yakubu Lawan Yarima a dai dai lokacinda yake kabar Shahadarsa ta kama aiki.
Allah ya bamu Nasara daga Sama har Kasa.#S4S DALA LG#

Sannu Da Zuwa Buhari

Tawagar yakin neman zaben Buhari a Kano

A Yau Buhari Newmedia Centre, Karkashin Jagorancin P. A Bashir Ahmad Akan Gabatar Da Taron Jadadda Goyon Bayan Babanmu Mai Girma Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.Sannan Da Tattaki Zuwa Kasuwani Da Jin Raa’yin Yan Kasuwa Akan 4+4.
Allah Ya Bamu Nasara A. P. C Daga Sama.
Haka Kuma Muna Gayyatar Al’ummar Jihar Kano Zuwa Taron Kaddamar Da Yakin neman Zaben Mai Girma Shugaban Kasa Da Kuma Duk Yan Takarkarun mu Na Jam’iyar APC Daga Sama Har Kasa.
Sako Daga Abdullahi Ahmad Tadada
Asst Secretary Kano State BNMC

YAKIN NEMAN ZABE

Buhari zai ziyarci jihar Kano

#S4S2019

Mun sami rahoton cewa, yayin da guguwar yakin neman zabe ke ci gaba da kadawa, shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Alhamis 31 ga watan Janairu, zai ziyarci jihar Kano domin girgiza magoya bayan sa yayin da babban zaben kasa ya gabato.

Labaran da muka samu da dumi-duminsu sunce, jami’an tsaro sun kara tsaurara matakan tsaro a ciki da wajen Kano, a baya ‘yan siyasa sunyi ta rade-radin cewa, shugaba Muhammad Buhari ba zai ziyarci Kano ba.

Muna fata za’ayi taro lafiya a gama lafiya.

Daga Na’Allah Raheemeeb

KWAMITIN KAMFE NA MALLAM IBRAHIM SHEKARAU

SANARWA TA MUSAMMAN

Daga Director General na Neman zaben Mai Girma Dr Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano

Drumar Maimansaleta

Sunayen Yan Kwamatoci
Allah ya bamu Nasara.

KURA GARIN NA’ALLAH

Talata 29/01/19

Rundunar Nasara ta Jam’iyyar Apc karkashin jagoranci Maigirma Gwamnan jahar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje da Tsohon Gwamnan jahar kano Dan Takarar Sanatan Kano ta Tsakiya suka sauka garin Kura/Madobi/Garun Malam.

Al’ummar Wannan yanki sun amsa kira sunce ranar zabe kawai suke jira zasu yi Apc daga sama har kasa 4+4 Buhari/Ganduje Shekarau4KanoCentral.

Mutan Kura Sunce Sai Baba Uban Abba

SAKON TAYA MURNA GA JAM’IYYAR APC

Sun ajiye jar tagiya

#S4S2019

Dubun dubatar mabiya darikar Kwankwasiyya ne a yau Talata 29/01/2019 suka jefar da jajayen hulunansu domin shiga Jam’iyyar APC a garin Madobi.

Wannan ya bude wani sabon shafi a siyasar Madobi inda ake ganin cewa gari ne na Maigirma tsohon Gwamna Rabi’u Kwankwaso kuma inda yayi kakagida.

Karbe wannan gari da Jam’iyyar APC ke shirin yi daga hannunsa, ba karamin ci gaba bane, duba da yadda Maigirma Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje yake kokarin bujuro da ayyuka irin wadanda takwaran nasa yakasa yiwa yan garin nasa.

Dubban jama’a ne suka halarci shaidar gani da ido yadda Karamar Hukumar Madobi ke shirin kubucewa Rabi’u Kwankwaso.

Daga Na’Allah Raheemeeb

KWARYA A GURBINTA

#GandujeSaiKai8

Gaskiyar magana maigirma gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje yayi abinda da yakamata yayi wajen sakawa titin karkashin kasar nan sunan mutumin daya bada gudunmawar sa sosai wajen tallafawa da kuma cicciba dukkan matasa dama duk wani dan asalin kano wato an saka mata sunan marigayi galadiman kano ALHAJI TIJJANI HASHIM

Baba ganduje muna godiya Allah ya saka maka da alkhairi

Sani Adamu Hotoro Secretary General
#S4S_Nassarawa

Allah Mungode

GODIYA DA BANGAJIYA

A madadin Shugabanni da jagororin jam’iyyar APC na Karamar hukumar Albasu

Muna mika sakon godiya da bangajiya ga dubun-dubatar Al’ummar da suka sami damar zuwa Karamar hukumar ta Albasu domin tare da rakiyar Mai girma Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje
Yayin da ya kai ziyarar ganawa da Al’ummar Karamar hukumar.

Wanda Wannan zuwa shine zuwa na 11 da Mai girma Gwamnan ya kawo Karamar hukumar

Da fatan kowa ya koma gidansa lafiya Allah ya huta gajiya ya kuma bar Zumunci
Mungode sosai

Sanarwa
Adam M Panda

GINA DAN ADAM

#S4S2019

“TAMU BA IRIN TASU BACE”

fb_img_15487185158821946952948.jpg

Abin nufi anan shine, mu mun yadda da dokokin da aka tsara, kuma muna binsu sau da kafa don gudanar da aikin jama’a saboda sanin cewa, Allah yana kishin bayinSa, shi yasa babbar manufarmu a wannan aikin amana da Allah ya dora mana, itace ta cicci6a marasa karfi a cikin al’ummarmu suma su tashi su zama mutane, su yi alfahari da cewa, su ma ‘yan Jihar Kano ne, ta hanyar tallafa musu, su sami madogara – H.E Mallam Ibrahim Shekarau (Sardaunan Kano)

GYARA KAYANKA

KOH DA TSIYA TSIYA

KOMAI TA FAMJAMA FAMJAM

Wadannan kalamai ne na kuskure kuma basu dace dakai ba ya maigirma dan sarki jikin sarki kuma zababben shugaban jam,iyyarmu ta APC na kano.

Ina fatan zaa kiyaye wajen furta kalamai makamancin wadannan domin gudun shiga hurumin ubangiji.

Allah ya taimaki jam,iyyar APC tun daga sama har kasa.

Ajingi, Albasu da Gaya

AIKI CIKIN MUTUNCI

Yau ma kamar kullum, kananan hukumomin Ajingi, Albasu da Gaya mutane sun fito domin fatan alkhairi ga tawagar Maigirma Gwamnan Kano Dr

Abdullahi Umar Ganduje da Maigirma Mallam Ibrahim Shekarau (Sardaunan Kano) dakuma ‘yan takarkarun APC na Jihar Kano

Dukkanin alamu suna nuna karfin magoya bayan da Jam’iyyar ta APC ke dashi yana karuwa a kowace rana, titi, lungu da sako ana fitowa domin yin tozali da gwanayen shugabannin mu.

#S4S2019

MATASA MASU KAYAN AIKI

TARON YAN KWANKWASIYYA YA RIKIDE ZUWA FASHI DA MAKAMI.

A jiya lahadi 27/1/2019 kungiyar kwankwasiyya da dantakarar gwamna na pdp suka gabatar da taron yakin neman zabe a karamar hukumar birni da kewaye a mazabar gandu kusa da trade fair, amma abin mamaki da bakin ciki bayan kammala taron yan qungiyar kwankwasiyyar suka farwa mutane masu wucewa a titi. da masu sayar da abinci
Abin nasu bai tsaya anan ba saida suka tare titin daya tashi daga dan’agundi zuwa gandu suna tare masu mota da adaidaitasahu suna yi musu kwacen kudade da wayoyi. kai hatta yara da suke sayar da kaya akan danja saida abin ya shafesu. domin akwai wani yaro mai sayar da pure water saida suka kwace ruwan suka shanye. kaii abindai babu dadin gani wlh, dan haka nake kira ga hukumomin tsaro yakamata su sanya ido akan wadannan yan kungiyar gurumaharaj din domin suna kawo barazana ga tsaron jihar kano, daga qarshe ina kira ga alumma dasu kauracewa zaben wadannan yankwankwasiyyar domin wlh mulkinsu babu alheri ga mutanen kano.

ALJANI YA BAYYANA AMATSAYIN BABBAN BAKO‼️

ALJANI YA BAYYANA AMATSAYIN BABBAN BAKO‼️

Ajiya a wajan taron Kwankwasia Aljanu sun Bayyana amatsayin manyan baki na musamman a wajan taron Kwankwasia, Ba mamaki daga India suke!
Wannan yake nuna cewar wakilin Shedanu ya Bayyana awajan, Duk inda kaji ance Shedanu sun bayyana kasan ko babu mutanen……
Wannan labari ya ishemu ta shafukan sada Zuminta yayinda suke posting kan cewar Aljanu sun bayyana babu adadi awajan hadi da wannan hotan.
Sakonmu ga dukkan yan Kwankwasia shine, Mu munyi imanin Allah ne me yi ba Aljanu ba, da ace dukkan Aljanun duniya ne zasu taru awajan taronku basu isa su baku nasara ba, Sai in Allah yaso, Domin shine mai ikon komai da komai shine mai caccanja abu buwa a duk sanda yaso, lillahi wahidun Qahharu, Bai haifa ba ba’a haifeshi ba.
Abin Takaicin ma shine yanda ‘Yan Kwankwasia suka dinga Kwace da sa duka da sara kan me uwa da wabi duk inda hanya ta hadasu, Misali a Gandun Albasa masu Shaguna rufewa suka dinga yi sabida abin Kwacen da ake da sa duka awani bangaranma har gidaje aka dinga rufewa Sabida Kwankwasia na operation kan me uwa da wabi.
Sutare mutun yana kan mashin suce bamu waya inyaki su kwace mashin ance a bakin digar jirgima Har adaidaita sahu suka kwace.

In baku manta ba a kwanakin Baya ba wanda yakai yan kwankwasia yada cewar su ba ruwansu da siyasar daba.
Wannan Masifa da me tayi kama antaba mulki dole ne, tanbayana ga dukkan yan kwankwasia yaransu da manyansu?

TANADIN SARDAUNA GA AL’UMMARSA

BANGARORIN DA MALAM IBRAHIM SHEKARAU ZAI BAWA MAHIMMANCI IDAN AKA ZABESHI SANATA.

#S4S2019

Malam Ibrahim Shekarau yace ” idan har Allah ya bashi damar zama sanatan Kano ta tsakiya, daya daga cikin bangarorin da zai bawa mahimmaci shine gina dan Adam, domin gina dan Adam shine gaba da gine-ginen hanyoyi da tituna.

Yace zaiyi duk mai yiwuwa yaga duk wani kudiri da zai gabatar a majalisar kudiri ne da zai samawa talaka saukin rayuwa da walwa, sannan zai hada kai da majalisar zatarwa ( Excutive) ya ga an samawa talaka rayuwa mai kyau”

Hakika wannan batu na sardauna haka yake domin yayi mungani a lokacin yana gwamna, talaka ya samu wal-wala an ragewa mutane talauci ta hanyoyi da dama, ta hanyar sama musu ayyuka da sana’oin dogaro da kai.

Da wannan muke fatan Allah ya bawa sardauna sanata domin cigaba da kyautatawa al’ummar Kano da Nigeria baki daya.

#S4S2019

Vote APC,
Vote Shekarau for Senator Kano Central

BICHI, BAGWAI DA SHANONO

#S4S2019

Bazaka yadda da idonka ba a lokacin da ka fara ganin wannan tururuwar al’ummah, amma daga karshe zaka fahimci lallai idanuwanka gaskiya suke nunamaka, saboda iyakar ganinka, mutane ne ke fiyowa domin Taron ganin tawagar Maigirma Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje da Maigirma Mallam Ibrahim Shekarau.

Taron yakai taro, anyi shi cikin jindadi, walwala da annashuwa, babu wanda aka zarewa makami domin a kwace masa waya.

Maimakon haka, sai wake-wake kakeji masu dadi sai kirarin da magoya baya ke yiwa shugabannin su, masamman lokacin da suka shigo cikin cikin taron dakuma lokacin da aka ambaci sunayensu kokuma suka mike domin gabatar da bayaninsu.

Anyi lafiya an gama lafiya

BICHI TA DINKE

Daga Karamar hukumar Bichi
Ana jiran karasowar Mai Girma Gwamnan Jihar Kano tare da Dantakarar Sanatan Kano ta Tsakiya Dr Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano

Daga Jibril Muhammad Na Tara

KWAMANDOJIN YAKIN SAMA

*KWAMATIN YANAR GIZO (Social Media) NA YAKIN NEMAN ZABEN MAL. IBRAHIM SHEKARAU A MATSAYIN SENATOR KANO TA TSAKIYA*

1. BELLO M. SHARADA *Director*
2. UZAIRU HUSSEIN *D-Director*
3. NASIRU ALKANAWY *Secretary*

*MEMBERS*

1- ABDULLAHI AHMED TADADA
2- YUSUF IBRAHIM MAI ATANFA
3- MUSTAPHA HASSAN
4- ISMAIL LAMIDO
5- AHMED GOGEL
6- USMAN SOLO
7- RABIU SENIOR
8- AUWALU RELATION
9- MUNNIR GURJIYA
10- SADIK YELLOW FAGGE
11- ALI ROMO
12- AUWAL DAN GWAMMAJA
13- ABUBAKAR ABDULLAHI DAWANAU
14- AUWALU BELLO
15- JIBRIN MUHAMMAD NATARA
16- NASIRU D UMAR ZUGAJI
17- KAMAL A BABA
18- ZAINAB ABDU FIKA
19- ZAHRAU IBRAHIM
20- USMAN ALI
21- MARAKISIYYA SANI RANO
22- ABDULLAHI BADAWI
23- AMINU ABBA MUHAMMAD
24- HAMISU TAJUDDEEN
25- HARUNA SHEKARAN GAMA
26- USMAN A. USMAN
27- UMAR FAROUK
28- ALIYU SARDAUNAN RIJIYAR LEMO
29- ABDULLAHI SHEKARAN KADAWA
30- KARAMALLAH HASSAN
31- NAFIU SANI SHANONO
32- MUHD SANI LABARAN (KALIFAN MALAM)
33- COMRADE YAKUBU ABDULLAHI

Allah yabada nasara a wannan tafiya

BELLO MUHAMMAD SHARADA

PDP DA APC A KANO CENTRAL

Hukumar zabe ta kasa wato INEC, ta saka ranar Asabat 16 ga Fabrairu 2019 a matsayin ranar da za a gudanar da zaben Sanata a Kano ta Tsakiya.

A wannan ranar za a hada wa mutum takardar zabe guda uku. Ta shugaban kasa wacce zai zabi shugaba Muhammadu Buhari ko waninsa, sai kuma ta Sanata wacce zai zabi Mallam Ibrahim Shekarau, ko waninsa. Sannan ta dan majalisar tarayya.

A Kano ta tsakiya akwai kananan hukumomi 15. Sune: Dala da Gwale da Nassarawa da Kumbotso da Kano Municipal da Tarauni da Ungoggo da Minjibir da Gezawa da Warawa da Dawakin Kudu da Kura da Madobi da Garun Mallam da Fagge. Duk wanda yake da kuri’a a wadannan kanananan hukumomi zai zabi Shekarau ko wani a matsayin sanata.

Yawan masu neman kujerar majalisar dattijai a Kano Central 30 ne a jam’iyyu 30. A cikinsu akwai mata uku da maza 27.Mutum uku cikinsu sun haura shekaru 60, biyar sun haura shekaru 50, sauran duka kasa da 50 suke, mafi kankantar shekaru a cikinsu shi ne Shehu Munzali dan jam’iyyar AGA shekararsa 33.

Manyan jam’iyyun da za a buga da su sune APDA wacce Muhammadu Abacha yake neman gwamna a cikinta. Sai APC mai dan takara tsohon gwamna Shekarau, sai PDP mai Ali Madakin Gini, dan majalisar tarayya mai ci daga Dala, sai PRP mai Sanata Rufa’i Sani Hanga.

Da Hajiya Laila Buhari da Ali Madaki da Shekarau da Sanata Rufa’i duk ‘yan cikin kwaryar birnin Kano ne.

Hukumar zabe ta yi wa mutum miliyan uku a Kano Central rijista. Akwai mazabu 172 a Kano Central, sannan akwai akwatunan zabe dubu 3713. A zabukan da aka yi a baya, na shekarar 1999 wanda ya yi nasara dan jam’iyyar PDP ne marigayi Kura Mohammed da kuri’a 193,895, wanda ya yi nasara a 2003 Sanata Rufa’i Hanga ya ci da kuri’a 288,708 a jam’iyyar ANPP, a 2007 Sanata Muhammad Bello ne ya wakilci Kano Central bayan ya lashe a ANPP da kuri’a 542,477, a 2011 Sanata Lado ne ya yi nasara da kuri’a 359,050 a jamiyyar PDP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso shi yake kan kujerar Kano central a majalisar dattiji bayan ya samu kuri’a 758, 383. Kwankwaso ne aka fi samun mafi yawan kuri’a a zabensa a cikin zabuka biyar da aka yi a Kano Central.

Yanzu zabe ya sake zagayowa, a ganina, wannan zaben za a yi shi ne a tsakanin Hon. Ali Madaki na PDP da Mallam Ibrahim Shekarau na APC, Madugun Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa ne ya tsayar da Ali Madaki, ita kuma APC ta baiwa Shekarau. Sauran jam’iyyu duk rakiya za su yi. Amma Allah ne mafi sani. A siyasa komai yana iya faruwa.

Tsayar da Ali Madaki yana daga cikin ragon azanci da Kwankwaso ya yi wa Dala da Kano. A majalisar tarayya tun daga shekarar 2011 Ali Madaki yana kokari, yana wakilci mai ma’ana, bai kamata rana tsaka a hankadar da shi daga kujerar ba. Shekarunsa ba su kure ba kuma ya fara zama dattijo a majalisar tarayya mai hawa biyu. Zai fi bada gudunmawa in ya ci gaba a wannan kujerar. Kano tana bukatar ‘yan majalisar tarayya gogaggu da sanatoci kwararru don bada wakilci mai nagarta da mutunci.

Yadda ya kamata shi ne mutanen Kano Central su zabi Mallam Ibrahim Shekarau ya maye gurbin kujerar Kwankwaso. Dattijo ne, majalisar ta dattijai ce, zai tarar da abokan aiki da yawa da ya sansu suka san shi, da za su hada gwiwa don taimakon Najeriya da mutanen Kano da Kano Central. Ya dace, ya cancanta kuma zai iya wakilci, saboda guri ne na lallami da lumana da saukin kai da tsantsar dimokuradiyya da bani-in-baka, duk ya iya su. Guri ne da ake tashi a yi bayani a gamsar da saura, Shekarau ya iya. Majalisa dakin doka da ka’ida ne, al’adarsa ce. Wakilin da zai wakilcin kwaryar birnin Kano ya zama wanda za a rika ganinsa ne a Abuja, sannan lokaci-lokaci zai zo Kano, hadimin al’umma da zai saurari koke ya kai gaba, sannan ya san halayyar mutanensa sarai. Duka Shekarau ya hada su.

A Kano Central a yi APC, a yi Shekarau, shi ne farar dabara.

NA BAR KU LAFIYA

Design a site like this with WordPress.com
Get started