Sanarwa ta Musamman Daga S4S

A Madadin Shugabani Da Magoya Bayan Kungiyar Shekarau 4 Senator (S4S). Muna Farin cikin Gayyatar Dukkan Masoya Mai Girma Gwamna Kano Khadimul Islam Dr Abdullahi Umar Ganduje Da Mataimakinsa Dr Nasiru Yusif Gawuna Tare Da Jagoranmu Sardaunan Kano Kuma Sanatan Kano Ta Tsakiya Mal Dr Ibrahim Shekarau Da Jam’iyar A. P. C, Zuwa Daurin Auren Yayan Daya Daga cikin Iyayen Wannan Kungiya Alh Salisu Indabawa.
1.Abubakar Salisu Indabawa Da Safiyya Dahiru Saleh
2.Bello Salisu Indabawa Da Husna Ridwan Ahmad
Wanda Za’a Yi Kamar Haka :-
Ranar :Asabar 27/7/2019
Lokaci :Karfe 11 Na Safe
Wuri:Massalacin Alfurqan Dake Alu Avenue.
Allah Ya Bada Ikon Halartar Ameen. Allah Ya Ya Sanya Albarka Da Alheri A Auren.
Mun Gode.

Shugaban S4S (Abdullahi Ahmad Tadada)
Sakataren S4S (Sani Bin Umar)

#SenIbrahimShekarauMedia

Buhari ya tura da sunayen Ministoci Majalisa

Ga cikakkun sunayen da jihohinsu kamar haka:

1. Abia: Dr. Ukechukwu Ogah
2. Adamawa: Muhammadu Musa Bello
3. Akwa Ibom: Sen. Godswill Akpabio
4. Anambra Dr. Chris N. Ngige
5. Anambra Sharon O. Ikeazor
6. Bauchi Adamu Adamu
7. Bauchi Amb. Mariam Y. Katagum
8. Bayelsa Timipre Silva
9. Benue Sen. George Akume
10. Borno Mustapha Baba Shehuri
11. Cross River Goddy Jedy – Agba
12. Delta Festus Keyamo, SAN
13. Ebonyi Dr. Ogbonnaya Onu
14. Edo Dr. Osagie Ehanire
15. Edo Clement IK Anade Agba
16. Ekiti Otunba Richard Adeniyi Adebayo
17. Enugu Geoffrey Onyeama
18. Gombe Dr. Ali Isa Ibrahim Pantami
19. Imo Emeka Nwajiuba
20. Jigawa Engr. Suleiman H. Adamu
21. Kaduna Zainab Shamsuna Ahmed
22. Kaduna Dr. Muhammad Mahmoud
23. Kano Sabo Nanono
24. Kano Maj. Gen. (RTD) Bashir Salihi Magashi
25. Katsina Sen. Hadi Sirika
26. Kebbi Abubakar Malami
27. Kogi Ramatu Tijjani
28. Kwara Lai Mohammed
29. Kwara Gbemisola Saraki
30. Lagos Babatunde Raji Fashola (SAN)
31. Lagos Sen. Adeleke O. Mamora
32. Nasarawa Mohammed H. Abdullahi
33. Niger Amb. Zubairu Dada
34. Ogun Arch. Olamilekan Adegbite
35. Ondo Sen. Tayo D. Alasoadura
36. Osun Rauf Aregbesola
37. Oyo Sunday Dare
38. Plateau Pauline Tallen
39. Rivers Rotimi Amaechi
40. Sokoto Muhammadu Maigari Dingyadi
41. Taraba Eng. Saleh Mamman
42. Yobe: Abubakar D. Aliyu
43. Zamfara: Sa’adiya Umar Farouk
Daga Umar Gaya

HALAYE GUDA 5 DA SUKA SA AKE GANIN IBRAHIM SHEKARAU A MATSAYIN ADALIN JAGORA

Daga Shehun Dashi:

Kyawawan halayensa da kyakyawar mu’amalarsa sunsa ya sufantu da halaye kamar haka : –

1 – Ganin girman dan Adam yanda baiya raina na kasa da ganin girman na gaba da tausayawa masu rauni a cikin al’umma.

2 – Yana neman sharawar masana, kuma yana karbar shawarar kowa dan yin amfani da da shawarar a gun da ya dace kan al’amurran da zasu kawowa al’umma cigaba.
3 – Bawa me haqqi Haqqinsa murukar yana karkashin jagorancinsa kama daga kan mabiya, da masu albashi, da yan kwangila, da masu Fansho, da sauran haqqoqi na al’umma.
4 – Gina al’ummar da suke karkashin kulawarsa da dukiyarsu, a fannin
* Tattalin arziqinsu,
* Kula da lafiyarsu
* Bunka cigaban iliminsu ta hanyar samar musu da wuraran karantarwa da kayan aiki tare da basu tallafin da zai taimaka musu wajen yin ilmin cikin sauki
* Da samar musu da yanayin da zai samar musu aiyukan dogaro da kai a fannoni kamar haka : –
– Noma da Kiwo
– Da jawo yan kasuwar da suke kasashe waje suzo su zuba jari a kasuwanni da masana’antun
– Da samar da tsarin da gwamnati zata samar da tallafin da zai habaka kasuwancin Misali : – Samar da tsarin bada tallafin Rago a lokacin Sallar laiya da kudin gero a lokacin Eidin kammala Azumin Ramadan
5 – Munufarsa ta ba kananan hukumomi damar baje basirarsu wajen samar da aiyukan raya kasa ga al’umomin da suke jagoranta.
Munufar Malam Shekarau ta sakarwa kananan hukumomi kudadansu ya yada arziqi a tsakanin gwamnatoci da al’umma.
Yan kasuwa da kananun yan kwangila sun sami arzuki silar wannan shiri, hakanan kananan hukumomi sun shigar da aiyukan raya kasa sako da lungunan birane da karkara, sannan sun taimakawa al’umma wajen basu tallafin ilmi, da dogaro da kai, da tallafin kula da lafiya

Wadannan halaye guda biyar da na ambata na tabbata ko makiyan MALAM IBRAHIM SHEKARAU sunai masa sheda kan abubuwan da na ammaba a sama

#SenIbrahimShekarauMedia

Sakacin Jami’an Tsaro a Najeriya

Matsalar tsaro a Najeriya har da sakacin jami’an tsaro, duba da yadda tsaro ke barazana a Najeriya, an sami wani mutum a filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Muhammad Airport dake Lagos, dare-dare akan fika-fikin jirgin AZMAN wanda ke dauke da matafiya daga Lagos zuwa Port Harcourt daidai lokacin da jirgin ke shirin tashi.

Wannan lamari, ba karamar barazana bace ga al’umma da dukiyoyinsu, ya akayi jami’an tsaro dake aiki a wannan filin jirgin sama sukayi sakaci haka ta faru, duk mutumin daya sami damar hawa fika-fikin jirgin sama, babu shakka zai iya kutsa kai cikin pilot cabin wato inda matuka jirgin suke aikinsu.

Babban abinda yafi daure kan jama’a shine, yadda hukumar kula da sauka da tashin jirage ta Najeriya karkashin wannan filin jirgin sama na Lagos ta tabbatar da cewa, wannan mutumin da aka kama kuma ake tuhumarsa a ranar Juma’a sun kamashi kwana biyar (5) a baya yana watangareriya a filin jirgin, amma duk da haka ba’a dauki kwararan matakan tsaro a kansa ba, aka sakeshi, gashinan sai da ya dawo domin cika burinsa.

Yakamata hukumomi su zage damtse wajen daukar mataki akan harkar da ta shafi tsaro komai kankantarta, domin yin biris da ita zai iya jawowa ta zama gagarima wacce zata iya kawo hasarar rayuka da dukiyoyi, Allah ya kiyaye.

#SenIbrahimShekarauMedia

Kungiyar Boko Haram Tayiwa Sojojin Najeriya Kwanton Bauna

Sojojin Najeriya sun tabbatar da kisan jami’ansu masu mukamin kanal da kaftin a wani kwanton bauna da ‘ya’yan kungiyar Boko Harma din suka yi musu a kan iyakar Borno da Yobe.

Kakakin rundunar sojojin ta bataliyon 212 kanal Isa shine ya bayyana haka.

#SenIbrahimShekarauMedia

Buhari ya gana da Lawan, Gbajabiamila

Da yammacin yau Laraba 17/7/2019 shugaba Buhari yana ganawa da shugaban Majalisar dattawa da takwaransa na wakilai Lawan da Gbajabiamila cikin sirri

Muna fatan ganawar tazamo alkhairi garemu da kasa baki daya.

#SenIbrahimShekarauMedia

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Babban Mai Shari’a na Kasa

Yanzu haka majalisar dattawan Najeriya tana gudanar da tantance babban mai shari’a na kasa a zauran majalisar.

A satin daya gabata ne Shugaban Kasa Buhari ya mika da sunan mai shari’a Tanko Muhammad zuwa ga majalisar domin tantanceshi duba da yadda majalisar alkalai ta Najeriya ta amince da ingancinsa, wannan yafaru ne bayan bashi rikon kujerar a yayin da aka dakatar da tsohon babban mai shari’a Chief Justice Walter Onnoghen bisa laifin kasa bayyana kadarorinsa.

#SenIbrahimShekarauMedia

GAYYATA ZUWA RAKIYAR SHIGA OFIS DA KAMA AIKI

Amadadin duk yan Uwa da abokan Arziki ana gayyatar Masoya zuwa rakiyar Mai girma sabon MD na Radio Kano Am/Fm Alh Ghali Sadeeq zuwa karbar aiki bisa wannan nadi da Mai Girma Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yayi masa muna gayyatar dukkan Masoya musamman Sardaunawa zuwa wannan rakiyar kama aiki wanda zai kasance kamar haka:-

Rana:- Alhamis 18/7/2019
Wurin Haduwa:- Sabuwar Kofa Rumfa College
Wuri:- Gidan Radio Kano
Lokaci:- 10 na safe

#SenIbrahimShekarauMedia

Makiyaya ku dawo Arewa inda za ku sami tsaro

Dattawan Arewa sun gargadi makiyaya su kauracewa kudancin Najeriya sakamakon salwantar musu da rayuwa da dukiyoyi da ake yi a can.

Shugaban wannan kungiyar ta dattawan Arewa (NEF) Prof Ango Abdullahi shine ya bayyana haka a yayin ganawa da ‘yan jarida a Abuja ranar Talata 16/7/2019.

Kungiyar tace makiyayan su gaggauta dawowa Arewa inda rayuwarsu da dukiyoyinsu zasu kasance cikin tsaro kamar yadda kowane dan Najeriya yake zuwa duk inda yaga dama ya zauna cikin walwala batare da tsangwama ba.

#SenIbrahimShekarauMedia

SAKON TAYA MURNA ZUWA GA ALH. GHALI SADIQ DAGA #S4S

A madadin jagorori da kuma shugabannin #S4S ta jiha karkashin jagorancin Abdullahi Ahmad Tadada da kuma sauran shugabannin kananan hukumomi muke amfani da wannan dama domin taya Alh. Ghali Sadiq bisa nadashi sabon MD na gidan rediyon Kano da mai girma Gwamna yayi.

Allah ubangiji (S.W.T) yayi masa jagora yayi riko da hannyensa. Allah ubangiji ya kauda dukkannin abin ki. Haka nan muna sake yin amfani da wannan dama domin yin addu’a ta musamman ga ainihin dukkannin shugabanninmu tinda sama har kasa da sauran dukkannin jagorori na jam’iyyarmu ta APC tin daga sama har kasa. Allah yayi musu jagoranci yayi riko da hannayensu domin samun nasarar gudanar da ayyuka domin ci gabanmu da ci gaban kasarmu gaba daya. Allah ya kara hada kawunanmu magoya baya. Allah ya kara mana lafiya da zaman lafiya a kasarmu da sauran kasashen yan’uwa musulmi na duniya.

Announcer:-

Basheer Basardaune,
State P.R.O #S4S
16/7/2019.

#SenIbrahimShekarauMedia

Ganduje ya sake nada wasu mukamai

Ga sunayensu kamar haka:

1 – Abdalla Pakistan – Shugaban Hukumar Alhazai ta jihar Kano

2 – Aliyu Musa Aliyu – Darekta Janar na Hukunar Hisba

3 – Halima Rabi’u Abdullahi – Babban Sakatariya na Hukumar Ilimi na Bai ɗaya.

4 – Gali Sadiq – Shugaban gidan Radiyon Jihar Kano.

5 – ‎Ibrahim Bichi – Babban Sakataren Ɗakin Karatu na Jihar Kano

‎6 – Sagir Sadisu Buhari – Darekta Janar na ma’aikatar Bincike da Adana.

7 – Lawan Sabo – Babban Manajan gidan jaridar ‎Triumph

‎8 – Sa’a Ibrahim – Darekta Janar gidan Talabijin din Abubakar Rimi (ARTV)

9 – Jibrilla Mohammed – Babban Manajan Kamfanin kula da kadarorin jihar Kano.

‎10 – Ibrahim Galadima – Shugaban Hukumar Wasanni na jihar Kano.

11 – Sakina Yusuf – Shugaban Kotun sauraren ƙararrakin matsalolin Hajji.

#SenIbrahimShekarauMedia

Hon Ghali Sadeeq MD Radio Kano

Muna mika sakon taya murna ga Hon Ghali Sadeeq, akan dana shi MD Radio Kano da maigirma Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yayi, Allah ya taya riko.

Sako daga S4S

#SenIbrahimShekarauMedia

Samun Wakilci Na Gari

A Yau Sardaunan Kano, Senator Dr Ibrahim Shekarau Ya Nuna Goyon Baya Akan Ci Gaban ilimi Da Amfani Da Na’ura Mai kwakwalwa a Makarantun Primary Har Secondary.
Muna Godiya Ga Kulawarka A Kan Ci Gaban Ilimi.

Sako Daga S4S

An dauke Wutar Lantarki a New York

A karo na farko cikin shekaru arba’in an sami daukewar wutar lantarki a New York ta kasar Amurka

#SenIbrahimShekarauMedia

Ameen Yaa Rabbal Alameen

👏🏻Ya Allahu
👏🏻Ya Rahamanu
👏🏻Ya Rahimu
👏🏻Ya Maliku
👏🏻Ya kuddusu
👏🏻Ya Salamu
👏🏻Ya Muminu
👏🏻Ya Muhaiminu
👏🏻Ya Azizu
👏🏻Ya Jabbaru
👏🏻Ya Mutakabbiru
👏🏻Ya Haliku
👏🏻Ya Bari’u
👏🏻Ya Musawiru
👏🏻Ya Gaffaru
👏🏻Ya Kahharu
👏🏻Ya Wahabu
👏🏻Ya Razzaku
👏🏻Ya Fattahu
👏🏻Ya Allimu
👏🏻Ya Qabiru
👏🏻Ya Basidu
👏🏻Ya Rafi’u
👏🏻Ya Mu’izzu
👏🏻Ya Muzillu
👏🏻Ya Sami’u
👏🏻Ya Basiru
👏🏻Ya Hakamu
👏🏻Ya Adalu
👏🏻Ya Ladifu
👏🏻Ya Khabiru
👏🏻Ya Halimu
👏🏻Ya Azimu
👏🏻Ya Gafuru
👏🏻Ya Shakuru
👏🏻Ya Aliyu
👏🏻Ya Kabiru
👏🏻Ya Hafiyu
👏🏻Ya Mukitu
👏🏻Ya Hasibu
👏🏻Ya Jalilu
👏🏻Ya Karimu
👏🏻Ya Rakibu
👏🏻Ya Mujibu
👏🏻Ya wasi’u
👏🏻Ya Wadudu
👏🏻Ya Hakimu
👏🏻Ya Mujidu
👏🏻Ya Ba’isu
👏🏻Ya Shahiydu
👏🏻Ya Hakku
👏🏻Ya wakilu
👏🏻Ya Kawiyyu
👏🏻Ya Matinu
👏🏻Ya Waliyyu
👏🏻Ya Hamiydu
👏🏻Ya Muhsiy
👏🏻Ya Mubdi’u
👏🏻Ya Mu’iydu
👏🏻Ya Mumitu
👏🏻Ya Hayyu
👏🏻Ya Kayyumu
👏🏻Ya Wajidu
👏🏻Ya Majidu
👏🏻Ya Wahidu
👏🏻Ya Ahadu
👏🏻Ya Samadu
👏🏻Ya Kadiru
👏🏻Ya Muktadiru
👏🏻Ya Makaddimu
👏🏻Ya Muwakhiru
👏🏻Ya Auwalu
👏🏻Ya Akhiru
👏🏻Ya Zahiru
👏🏻Ya Badinu
👏🏻Ya Waliyyyu
👏🏻Ya Muta’ali
👏🏻Ya Barru
👏🏻Ya Tawwabu
👏🏻Ya Muntakimu
👏🏻Ya Afuwwu
👏🏻Ya Ra’ufu
👏🏻Ya Malikal-Mulki
👏🏻Ya Zulijalali-Wal ikrami
👏🏻Ya Muksidu
👏🏻Ya Jaami’u
👏🏻Ya Ganiyyu
👏🏻Ya Mugni
👏🏻Ya Mani’u
👏🏻YaDarru
👏🏻Ya Nafi’u
👏🏻Ya Nuru
👏🏻Ya Hadi
👏🏻Ya Bafi’u
👏🏻Ya Baki
👏🏻Ya Warisu
👏🏻Ya Rashidu
👏🏻Ya Saburu.
🙏Allah dan girmanka dan kyawawan sunayanka, Allah dan buwayarka, Allah dan soyayya da kaunar da kakeyiwa Annabi Muhammadu SAW ka biya mana bukatunmu na alkhairi.

Allah yasa alkhairi Sardauna

Daga Jibril Muhammad Na Tara

LAHADI
Mai Girma Sanatan Kano ta Tsakiya Dr Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano Ya daura auren kanwarsa dake Gunduwawa.
14/07/2019

Qalubale gareku shugabanni

A duk fadin kasata Najeriya ga QALUBALE tun daga kan zababban kansila, Shugaban karamar hukuma, dan majalisar jiha, dan majalisar tarayya, dan majalisar dattijai, mataimakin gwamna, gwamna, mataimakin shugaban kasa da shugaban kasa.

Akwai wanda yana kan kujerarsa ta wannan mulki ya halarci janaza yayiwa gawar sallah sannan ya ja gaba zuwa makaburi aka suturta gawar dashi?

Karku manta cewa, gawar bata mahaifinsa bace, bata mahaifiyarsa bace, bata matarsa bace, bata dansa ko ‘yarsa bace, bata shakikinsa bace, bata amininsa bace, illah dai gawace ta musulmi dan uwansa a musulunci.

Ku duba kuga cikakkun bayin Allah, masu yi domin Allah, wadanda suke kallon ranar gobe kiyama fiye da duniya, wadanda basa kallon abinda zasu tara a cikin duniyar.

Irin wannan halin na Senator Ibrahim Shekarau CON Sardaunan Kano ya isa misali a fadin Najeriya, wallahi soyayya ga irin wannan bawan Allah babu da na sani cikinta, haka kuma kwaikwayon ayyukansa wajibine ga sauran mabiya da shugabannin wannan zamani.

#SenIbrahimShekarauMedia

Allah yaba Najeriya sa’a

Hamshakin mai kudin nan, dan asalin Jihar Kano a Najeriya Aliko Dangote, yasha alwashin biyan zunzurutun kudi har dalar Amurika dubu hamsin ($50,000) akan duk wata kwallo da ‘yan wasan Najeriya Super Eagles suka sa a zare yayi cigaba da wasan da zasu kara tsakaninsu da takwararsu ta kasar Algeria.

Shima takwaransa mai tashen kudi, wato Femi Otedola, yace zai bada zunzurutun kudi har dalar Amurika dubu ashirin da biyar ($25,000) akan kowace kwallo da ‘yan wasan na Najeriya suka zura a ragar kasar Algeria.

A yau ne da misalin karfe takwas na dare (8:00PM) agogon Najeriya, za’ayi wannan karan batta na kusa da na karshe tsakanin Najeriya da Algeria, inda kungiyar kwallon kafa ta Najeriya Super Eagles suka sami damar shiga wannan mataki baya da suka doke takwararsu ta kasar South Africa da ci 2 da 1.

Kafin wannan lokaci ‘yan wasan kasar Senegal zasu kece raini tsakaninsu da kasar Tunisia da misalin karfe biyar na yamma (5:00PM) agogon Najeriya.

Muna bukatar dokokin da zasu kawo karshen zamba cikin aminci

Ina kira ga ‘yan majalisu suyi gaggawar kawo dokar da zatayi hukunci bai daya ga masu sace mutane suyi garkuwa dasu da maza masu hallaka matansu da mata masu hallaka mazan su.

Ya zama wajibi ayi gaggawar kawo wannan doka domin abin yafara zama ruwan dare a tsakankanin mutane, matasa da magidanta, zura ido da mutane keyi suga irin hukuncin da za’ayiwa wadanda aka kama da wadannan laifuka bai isaba, sai suntashi sun tunkari majalisun dokoki domin gabatar da korafinsu akan tabbatar da wannan doka.

A gaskiya abin yayi yawa, kuma har zuwa yanzu bamuji wani babban hukunci da aka gabatar akan ire-iren wadannan masu danyan aika-aika ba, akwai yaudara a cikin irin wannan hali kokuma nace zamba cikin aminci.

A yayin da mace ta amince da mijinta, a matsayin mai kareta daga koda cizon sauro ne, haka kuma miji ya amince da matarsa a matsayin mai kareshi daga cizon cinnaka, kokuma yaron gida wanda aka aminta dashi a matsayin wanda zai dauki dan maigida zuwa makaranta ya dawo dashi gida lafiya.

Amma abin takaici, miji ya kashe matarsa duk da irin kalaman soyayyar da yayi mata har ta amince ta aureshi, haka kuma mace ta kashe mijinta duk da irin alkawarin zata rayu dashi har mutuwa, kokuma yaron gida da ake bashi ci da sha da sutura da ilimi amma ya dauki dan maigida ya sace ko ya kashe, gaskiya sai al’umma da gwamnati sun mike tsaye wajen hana yaduwar wannan mugwayen abubuwa dake tumbatsa cikin al’umma.

#SenIbrahimShekarauMedia

Sanata Ibrahim Shekara CON Ya Dawo

Yanzu Sanata Ibrahim Shekarau ya shigo fadar Mundubawa inda ya dawo daga Abuja bayan halartar zaman majalisar da yayi na wannan mako.

Sardauna dan kwarai, daga aiki a Abuja sai gida Kano domin cigaba da sadar da zumunci da sauran al’umma na daure-dauran aure ta’aziyya da janaza da kuma ganawa da ‘yan siyasa manya da yara.

Allah ya kara lafiya dai Sardauna, ‘yan Kano muna goyon baya.

#SenIbrahimShekarauMedia

Kotun Daukaka Kara Tayi Watsi Da Tuhumar Da Akewa Shugaba Buhari

Wata kotun daukaka kara tayi watsi da karar da akakai shugaba Buhari na rashin takardar sakamakon halartar makaranta.

#SenIbrahimShekarauMedia

Mune Da Alhakin Tarbiyyar Yaranmu

Matasa sun zarme wajen son kudi da holewa da mallakar manyan wayoyi ta gurbatacciyar hanya, inda suka shiga kwace ta hanyar barazana da muggan makamai a tsakar rana akan titinan Jihohinmu, idan suka tare mutum domin su kwace masa waya kuma yayi inda-inda yanzu sai su buga masa karfe mai kaifi, su kwace wayar, koma su kasheshi su dauke wayar.

Kullun ana fadakar dasu amma abin kamar wutar daji sai kara ruruwa takeyi, abin mamaki shine, yanzu haka matasan sun shiga mataki na gaba wajen sake sabuwar sana’ar garkuwa da yara kanana domin neman kudin fansa, a irin wannan yanayi wasu matasa su 3 sun sace wani yaro ta hanyar yaudarasa a matsayin wadanda yasani kuma sukayi garkuwa dashi suka nemi iyayansa su biya manyan kudade domin maidashi garesu.

A cigaba da wannan haline sukayiwa yaron asarar ransa inda suka kasheshi kuma suka binne, amma a kwarewar bincike na ‘yan sanda suka kamasu kuma suka kwakwalo gawar yaron a inda suka binneshi.

A gaskiya, matasa sune manyan gobe, idan suka gurbace da neman siddan ta kowace hanya domin su sami abinda zasuyi bushasha da kudi da manyan wayoyin hannu da sutura da kashewa ‘yan mata batare da sunsan wahalar nema da samu ba, to lallai matsalolinmu sun kama hanyar da bazamu iya gyaruwaba, yazama dole iyaye su rage shagwaba ‘ya’yansu, su bari doka yayi aiki akansu, soyayyar da muke nunawa garesu tasa basuda wani katabus wajen neman abin kansu ballantana su taimakawa iyayensu ko yan’uwansu koma kasarsu.

Kowane lokaci burinsu su samu a sama,

#SenIbrahimShekarauMedia

Babu Maganar Kara Kudin Man-Fetur – NNPC

Hukumar samar da man-fetur a Najeriya NNPC ta bukaci al’umma suyi watsi da wata jita-jitar dake zagayawa cewa zata kara kudin mai.

Wannan ba gaskiya bane, kudin mai yananan kamar yadda akasani N145, kamar yadda hukumar tace, shugaban hukumar ta NNPC Mele Kyari, ya fadawa shugaban majalisar dattijai Ahmad Lawan cewa, ana sayar da mai a Najeriya kasa da saurarn makwaftan kasashen Africa a yayin ganawarsu a zauran majalisar, baya nufin kara kudin man-fetur din.

#SenIbrahimShekarauMedia

Inyamuri (IGBO) A Siyasar Najeriya

Matukar inyamuri yana bukatar sake karbuwa a siyasar Najeriya to lallai sai ya gina gada ta daidaitawa da ‘yan Arewa da Yarabawa, ba wai ya gina shinge tsakaninsu ba inji Churchill Okonkwo.

Yin murna da dariya ga ‘yan Arewa maso Yamma yayin da ibtila’in kashe-kashen dake faruwa a can da kuma kiran Yarabawa da sunaye daban-daban na batanci bazai kai inyamurai ko ina ba a siyasance.

Zamu dau mataki akan kungiyar Shi’a – Shugaban ‘Yan sanda na Najeriya

Babban sifeton yan sandan Najeriya yasha alwashin daukar kwararan matakai akan kungiyar Shi’ite da suka kai wa jami’ansa hari.

#SenIbrahimShekarauMedia

Najeriya Ta Shiga Matakin Na Gaba

Kungiyar kwallo kafa ta Najeriya Super Eagle ta doke takwararta ta kasar South Africa a gasar cin kofin Africa da ci 2 da 1 inda zata buga matakin wasa na biyun karshe a wasa na gaba.

Kotun sauraron korafin zaben shugaban kasa a Abuja – S4S

Yayin sauraron korafin zabe a Abuja inda Atiku Abubakar ke kalubalantar lashe zaben shugaban kasa da shugaba Buhari yayi a zaben da ya gabata.

Atiku Abubakar ya gabatar da shaidu a karon farko, wadanda zasu shaidawa kotu cewa ko shakka babu shine ya lashe zaben, nan take aka gabatar da shaida na farko mai suna Buba Galadima.

Yayi bayanin dangantakarsa da Buhari tun 1960 inda ya bayyanashi da mutumin kirki, jajirtacce kuma mai gaskiya, amma yabar tafiyarsa ne sakamakon ya kasa aiwatar da alkawuran zaben da aka zabeshi domin ya aiwatar.

Yayin da lauyoyi suka tambayeshi ko yana sane da ‘yarsa tana cikin gwamnatin? Ya amsa da cewa, ya sani, amma ‘yar tasa tafi kowane jami’in gwamnatin ta Buhari ilimi kuma har yanzu shima dan jam’iyyar ta APC ne kuma babu wanda ya isa ya koreshi tunda dashi aka kafata.

Shaida na gaba ya bayyana cewa, shi ma’aikacin da hukumar ta dauka domun gudanar da zaben ne, ya tabbatar da sunyi aiki da card reader kuma sun tura da sakamakon kai tsaye zuwa runbun tara bayanai na INEC inda sukayi amfani da wata lamba ta sirri da hukumar ta basu domin tura sakamakon zaben.

Da lauyoyi suka tambayeshi ko zai fadawa kotu wannan lambar ta sirri da aka basu domin tura sakamakon zaben? Sai yakada baki yace, ya manta lambar.

Sai shaida na gaba, inda ya tabbatarwa da kotu cewa a inda aka turashi yayi aikin zabe, ba’ayi zaben ba, amma sai gashi an bayyana sakamakon zaben a yayin bayyana sakamakon zabe na jihar,

Da lauyoyi suka tambayeshi ko shi da kansa ya sami uzirin jefa tasa kuri’ar? Nan take ya amsa da cewa yayi nasa zaben.

Sai shaida na gaba, inda shima yace sun tura da sakamakon zabe cikin runbun tara bayanai na hukumar zaben ta hanyar card reader.

Da lauyoyi suka tambayeshi wace rana akayi zaben shugaban kasa? Nan take yace bazai iya tunawa ba.

Lauyoyi da shaidu da alkalai aci gaba da gashi, suya sai ranar sallah.

Kato Yayi Shigar Mata Ya Kutsa Kai Makarantar Mata Ta FCE Kano

Wani kato yayi shigar mata yana kokarin shiga makwancin mata a FCE Kano, a lokacin da jami’an tsaro a makarantar suka sha jinin jikinsu cewa, wannan baiyi kama da tafiyar mata ba kuma damtsensa da kafafuwansa shima irin na maza ne.

Nan take suka tsareshi domin tuhumarsa, sai kuwa gashi hakan ta tabbata cewa, namiji ne yayi shigar mata, bayan dogon bincike sun mikashi ga hukumar ‘yan sanda domin cigaban da tuhumarsa.

#SenIbrahimShekarauMedia

Zamu Daukaka Darajar Asibitocin Sabbin Gundumomin Masarautu – Ganduje

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje yasha alwashin daukaka darajar asibitocin sabbin masarautun gargajiya na gundumomi hudu (4) daya assasa a Jihar Kano.

Yayi wanna jawabi a gaban Sarkin Rano Mai martaba Alhaji Tafida Abubakar ranar Asabar 6/7/2019 inda yakai masa ziyarar ta’aziyya na rayuwar dansa Alhaji Aliyu Tafida.

Gwamna Ganduje, yace, daukaka darajar asibitocin zai rage da saukaka zirga-zirgar marasa lafiya zuwa birni domin neman magani, irin wannan kawo cigaba kusa da jama’a shine dalilin assasa wadannan masarautu.

A bayanin maida martani, Sarkin Rano, Alhaji Abubakar Tafida Autan Bawo, yayi godiya ga Gwamna Abdullahi Umar Ganduje da Gwamnatinsa wajen maida hankali na farfado da masarautun guda hudu (4) domin cigaban al’ummar yankunan nasu.

#SenIbrahimShekarauMedia

Abdullahi Shekaran Kadawa Ya Tsere Sa’a

Maigirma Sardaunan Kano, Senator Ibrahim Shekarau CON ya halarci daurin auran daya daga hadimansa a yanar gizo kuma coordinator #S4SUngogoLG, Abdullahi Shekaran Kadawa, wanda aka gudanar ranar Lahadi 7/72019.

Muna fatan Allah yasa albarka, ya bada zaman lafiya da hakuri da juna.

#SenIbrahimShekarauMedia

Design a site like this with WordPress.com
Get started