
Magana ta gaskiya kamar yadda naji wasu marubuta suna danganta sarautar gargajiya masamman a Jihar Kano da siyasa na amince hakane amma lokaci ake dubawa, a baya kamar yadda akayi bayani tun daga 1955 idan muka duba dole sarakuna su kasance ‘yan siyasa duba da irin hurumin aikinsu masamman na rike madafun iko.
A wancan lokacin, sarakuna keda alhakin shugabantar Native Authority (NA) inda ‘yan sanda, gidan yari, malamai na makarantu, da sauransu ke karkashin ikonsu amma tunda aka fara mulkin dimokaradiyya ta jamhuriya ta farko aka kwace wadannan madafun ikon a hannun sarakuna kuma aka haramta musu shiga sabgar siyasa inda suka zama iyayen kasa kawai, ma’ana kowa nasu ne babu banbanci.
Amma wancan burbushin sarautar da suka dafa na madafun iko a baya, shine yake tasiri wajen tsomala baki a bayan fage duk da sunsan haramun ne a garesu, matsalar shi wannan Sarkin na Kano zakewa da fitowa fili yana yakar gwamnatin da ludayinta ke kan dawo kuma wacce take biyansa da majalisarsa albashi harma da bashi wasu rarar kudade na tafiyar da masarautar.
Shi Sarki fa idan muka duba kamar ma’aikacin gwamnati ne a irin wannan tsarin wanda duk gwamnatin da tazo zata tafi dashi, don haka yazama dole ya sunkuyar da kansa yayi biyayya yayi aiki tare da gwamnatin da take kan gadon mulki, ba kokarin yin aiki da gwamnan da mulkinsa ya shude ba, yin haka nuna kiyayya ne karara ga Gwamnatin da take kan mulki, na tabbatar koma waye bazai dauke kansa ya zuba ido ana takashi ana lakuce masa hanci, ana wofantar dashi ta hanyar kokarin ganin bayansa daga kujerar mulkisa ba.
Kamar yadda marubuta suka tabbatar da rashin adalcin da Kwankwaso yayi na kakabawa al’umma abinda basa bukata bai kamata musaka hannun Ganduje cikin wannan danbarwar ba, duba da cewa, a lokacin bashi da ta cewa a matsayinsa na mataimakin gwamna wanda tsarin mulkin ma bai tantance masa cikakken aikinsa na mataimaki ba, kuskure ne mu sakoshi a matsayin dashi aka nada Sarki Sunusi Lamido Sunusi II.
Shekaru hudu suka shafe tare akan gadon mulki, duk da cewa masarautar tana ta ciwa gwamnan fuska bai daga ido ya duba ba, har bayan shekaru 2 sannan ya shafa kan Sarkin kafin a dawo a daidaita, kasancewar an daidaita wane dalili kuma ya dawo da wancan cin fuska a daidai wannan lokaci?
A fahimtata, tunda wancan daidaitawa da akayi ta fari bata isa masarauta ta daina ciwa gwamna fuska ba, banyi zaton daidaitawar da aka sake yi a halin yanzu zata dakatar da Sarki daga abinda ya sabayi ba, na tabbatar nan da shekaru biyu zuwa uku masu zuwa matukar Sarki yana gadon mulki sai ya sake ciwa gwamna Ganduje fuska, kuma zai sake yin kokarin hada kai da Kwankwaso da magoya bayansa domin suga sun cimma burinsu na hana duk wani dan takarar jam’iyyar APC da ta tsayar na gwamna a wannan Jiha ta Kano.
You must be logged in to post a comment.