Alh Abdullahi Ahmad Tadada S4S State Chairman Kenan

Daga Amir Yakson:

Gyara kimtsi dakyau!!!

Alh Abdullahi Ahmad Tadada S4S State Chairman Kenan yayin da yake mika Gaisuwa ga Mai Girma Sardaunan Kano.
Kai da ganin gaisuwar kasan akwai Mutun taka da Girmamawa Tsakin Mai Girma Sardaunan kano da Chairman Abdullahi Ahmad Tadada.
Zama da Mutane lafiya yayi anfani aci gaba da biyayya Chairman za aga Alherin hakan agaba insha Allah.
Harkulun fatanmu da Addu’armu Allah ya aiko da babban rabo Chairman Ameen🙏

#SenIbrahimShekarauMedia

Kullum A Cikin Hidimar Jama’a Yake.

Daga Abdullahi Ahmad Tadada:

Kullum A Cikin Hidimar Jama’a Yake. Kuma Tun Da Aka Zabe Shi A Majalisar Dattawa Yake Bayar Da Gudunmawar Dan Ci Gaban Al’umar Najeriya, Arewa, Jihar Kano Da Kuma Sanatorial Dinsa. Dan Haka Ya Zama Daya Tamkar Da Dubu.
A Saboda Haka Na Zabe Shi A Matsayin GWARZON SHEKARAR 2019.Wato Sanatan Kano Ta Tsakiya Mal Dr Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano. Shine Gwarzan Shekara Ta, Kaifa /kefa?
Sako Daga S4S

#SenIbrahimShekarauMedia

Sako daga #S4S

Daga Abdullahi Ahmad Tadada:

Godiya Ga Allah Da Ya Kawo mu Karshen shekarar 2019.Allah Ya Gafartawa Wadanda suka Rigamu Gidan Gaskiya, ka bawa marasa lafiya, lafiya. Ka yi mana Gafara Na Zunubanmu.
Ya Allah Ka Hadamu Da Alheri Sabuwar Shekarar Da Zamu Shiga Ta 2020 lafiya. Ya Kara Mana Arziki, Sutura Da Daukaka A Cikin Ta. Ka Tsare mu Da Dukkan Sharri.
Allah Ya Jikan Dukkan Musulmi Baki Daya, Ya Bawa Marasa lafiya Na Gida Da Asibiti lafiya.
Ina Yi Mana Barka Da Sabuwar Shekarar 2020 Nan Da Yan Kwanaki.
Sako Daga S4S

#SenIbrahimShekarauMedia

Sakon Ta’aziyya Daga Sen Ibrahim Shekarau Media

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI’UN!

A daren jiya Talata 17/12/2019 Allah yayiwa Mallam Haruna Ibrahim Panshekara rasuwa, ma’aikaci a hukumar bada ruwa ta Jihar Kano, WATER BOARD.

Mallam Haruna Ibrahim, mutumin kirki, mai son addini da girmama jama’a, wallahi nidai munfi haduwa dashi a masallaci. Idan kuma yazo majalisar mu bai wuce zancan Sardaunan Kano ba, saboda masoyin ne na gaske.

Tuni akayi janazar sa a yau laraba 18/12/2019. Muna addu’ar Allah SWT yai masa rahama ya yafe dukkanin kusa kuransa, Allah kasa Annabi Muhammadu SAW yasan da zuwan sa.

Ibrahim Ali

Sakon taya murna ga abokina Alh Bello Haruna Umar

A yau Asabar 14/12/2019 Maigirma Sanatan Kano Ta Tsakiya Dr. Ibrahim Shekarau CON Sardaunan Kano ya jagoranci daurin auren ‘ya’yanmu Muhammad Bello Haruna da amaryar sa Aisha Abdullahi Adamu wanda aka gudanar a No 789 Abdullahi Dabo Street, unguwar Tudun Maliki.

Muna godiya da manyan baki da suka halarta da wadanda wasu uzirori basu basu dama ba, mungode da addu’oinku, muna addu’a Allah yaba Ango da Amarya zaman lafiya, kwanciyar hankali da karuwar arziki.

Ibrahim Ali Panshekara

SANARWA TA MUSAMMAN

GWAMNA GANDUJE YA NADA SARKI MALAM MOHAMMADU SUNUSI II. A MATSAYIN SHUGABAN MAJALISAR SARAKUNAN JIHAR KANO..

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da nadin Sarkin Kano Sunusi Lamido Sunusi a matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna a Jihar Kano a bisa damar da Gwamna ke da ita wajen nadawa na sabuwar dokar karin masarautu ta 2019.

Daga Cikin Majalisar Sarakunan akwai Mai Martaba Sarkin Bichi Alh Aminu Ado Bayero, Sarkin Karaye, Alh Dr Tafida Abubakar Autan Bawo,Sarkin Karaye Alh Dr Ibrahim Abubakar,Sarkin Gaya Alh Ibrahim Abdulkadir Gaya wanda suke a cikin dokar.

A cikin dokar yabada dama asaka Sakataren Gwamnati,Kwamishinan Kananan Hukumomi, dakuma Shugabannin Kananan Hukumomi dake Hedkwatan kowacce masarauta.

Sannan acikin yan Kwamitin akwai Masu Nadin Sarki Mutum 2 daga kowace masarauta cikin guda 5. Dakuma Babban Limami daga kowace masarauta dakuma hamshakin dan kasuwa daga kowace masarauta inda Gwamna yazabi Alh Dalhatu Abubakar alhamsad da Alh Auwalu AA Rano.

Hakazalika Dokar tabada dama a dauko wakilai daga Hukumar yan sanda, dana farin kaya dakuma civil defence dakuma mutane 2 da Gwamna yake da ikon zabensu inda yazabi Alh Nasiru Aliko Koki, sai Sakataren Majalisan Wanda za’a zabeshi daga Majalisar Sarakunan.

Dokar tabada dama Shugabancin yazagaya ko ina cikin shekaru 2 inda Shugabancin Sarki Sunusi yafara daga Yau Kuma ake umartarsa da ya fara kiran Taron Kaddamarwa nan take.

Daga Karshe Gwamna Ganduje yana Taya sabbin yan Majalisar Sarakunan Jihar Kano murna tare da Fatan zasu Yi kokarin ganin ansamu cigaba a Fannin masarautunsu dakuma sha’anin Tsaro.

Daga Abba Anwar.
Fassarawa Talba Dan Abba

#SenIbrahimShekarauMedia

Ganduje Ya Aikawa Majalisa Sabuwar Doka Don Kafa Masarautu Hudu

Ganduje Ya Aikawa Majalisa Sabuwar Doka Don Kafa Masarautu Hudu, Bayan Kotu Ta Kori Sarakunan

Daga Comr Abba Sani Pantami

Majalisar zartarwa ta jihar Kano ta amince da kudirin Emirate Council na shekarar 2019 wanda ya tanadi samar da karin Hadaddiyar Daular Emirate a cikin jihar.

Gwamnan ya yi wannan taron gaggawa ne a zauren majalissar, Gidan Gwamnati, Kano, ranar Lahadi da daddare.

A ranar 21 ga watan Nuwamba, wata babbar Kotun Kano wacce Mai shari’a Usman Na’Abba ke jagoranta ta rushe karin masarautun guda hudu tare da korar wasu sarakuna hudu na farko da gwamnatin jihar ta kirkira.

A ranar 8 ga Mayu, gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, ya amince da wata doka mai rikitarwa ta kafa wasu sarakuna hudu tare da sarakunan farko a Bichi, Rano, Karaye da Gaya.

Bayanan daga ciki sun fada wa DAILY NIGERIAN cewa gwamna ya fara gabatar da dokar amma an gabatar da shi ga majalisar ta hanyar wakili.

A bayyane don guje wa kuskuren abin da ya gabata, majalisa a wannan karon ta shirya lissafin zartarwa ga taron don ƙirƙirar masarautan.

Wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Mohammed Garba, ya fitar ta ce majalisar ta amince da samar da sabbin Emirates guda hudu wadanda suka hada da Rano, Gaya, Bichi da Karaye da kuma gabatar da shi ga majalisar dokokin jihar don daukar matakin da ya dace.

Da yake bayyana dalilin dagewar gwaminatin, Mista Garba ya ce wasu daga cikin wadannan Emirate din sun ma riga sun yi mulkin Kano a zamanin da, “yayin da kokarin farfado da su a jamhuriyya ta biyu ya yi gajere.”

Ya ce, yayin da majalisar ta ke tattaunawa sosai kan “tsawan shekaru goma na kafa karin Emirates a jihar tare da kokarin samar da ci gaba ga jama’ar sabuwar UAE, kuma an sanar da aikin game da bukatar samar da cibiyar gargajiya ta kusa da ita. mutane baya ga gudanar da saurin ci gaban tattalin arziki da tsaro a cikin jihar. ”

Bayanin ya ci gaba da nuna cewa gabatar da Karatuttukan Ilimin kyauta da na Wajibi a matakin Farko da Sakandare na bukatar taka rawar gani a cikin al’umma musamman cibiyoyin gargajiya don aiwatar da nasarar ta.

Kwamishinan ya yi nuni da cewa an yi kwaskwarimar kudirin dokar Emirate Council 2019 a cikin bukatun jama’a biyo bayan matakin da babbar kotun jihar Kano ta yi wanda ya soke dokar a kasa cewa mutum ne wanda ba dan majalisar ba ya gabatar da karar.

Majalisar, a cewar sanarwar, saboda haka, ta yi kira ga Majalisar Dokokin Jiha da ta gaggauta daukar mataki a kan kudirin dokar don amfanin jama’a.

#SenIbrahimShekarauMedia

Jami’ar RITMAN a Jihar Akwa Ibom zata karrama Sen Ibrahim Shekarau

A yau Asabar 30/11/2019 jami’ar RITMAN a Jihar Akwa Ibom ta shirya karrama Distinguish Sen Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano.

Inda ya sami kyakkyawan tarbo daga gwamnatin Jihar ta Akwa Ibom tare da dimbin yan rakiya wadanda suka hada da Gwamna, shugaban jam’iyya, kwamishinoni, Sanatocin Jihar Kano da manyan baki daga sassa daban daban.

#SenIbrahimShekarauMedia

An saki dalibin da dan majalisar Kano ya daure saboda rubutun ‘Facebook’


Kotun dake sauraren karar da dan majalisa mai wakiltar Madobia jihar Kano Ismaila Kabir ya shigar ya inda ya saka aka tsare wani dalibin jami’ar Kano mai suna Yahuza Tijjani ta sake shi a safiyar Alhamis.

#SenIbrahimShekarauMedia

Tsare dalibin jami’a Yahuza Tijjani

A wata faifan radiyo da aka dauka a wani hira da dan majalisar jihar Kano dake wakiltar Madobi, an ji shi kakara ya bugun kirji yana cewa Ko sarkin Kano Sanusi ba zai iya saka shi abu yayi ba.

A wannan faifai an ji Honarabul Isma’ila yana cewa babban jojin jihar Kano ne ya umarce Alkalin dake sauraren karar da ya shigar game da cin fuskar da yake zargin dalibi Yahuza dake karatu a jami’ar Bayero da yayi masa da ya ci gaba da tsare shi a gidan kaso har zuwa wani lokaci.

” Duk Madobi indan ana batun ga wane shegen kansa ne, wanda a baya zai iya yin duk abin da yaga dama kowa dai ya san haka yake amma wallahi tallahi babu mutum da zai yi mun haka ya ce zai ci lafiya.Wallahi da daga kaina ba zai kara ba.

” Saboda haka nake ganin wannan itace hanya mafi sauki tun da mu musulmai ne domin duk abin da ka aikata ka san kana da sakamako.Kuma wannan abun da na yi na tabbata har ga Allah ban zallunci Yahuza ba.

” Misali duk Kazafi-Kazafi da Yahuza ya ambato idan bulalla za a yi masa bulala nawa zai sha idan aka kwantar da shi?Sannan idan zan kai shi kotu na shigar da kara nawa Yahuza zai kashe domin bashi da yadda zai yi ya biya na.

” Ku saurari abin da nake gaya muku game da abin da Yahuza ya yi domin a rayuwa wani zai ga cewa an yi amfani da girmar kujeran sa ne domin ya dane Yahuza.Amma ni na sani ko bana kan kujera, ni ba sa’an Yahuza bane domin ko babu komai ka tursasa ni zan iya fito maka da miliyan 50 zuwa 100. Amma Yahuza idan ka matsa masa akan 100,000 sai duniya ta ji. Ka ga ko a nan ma na fi karfin sa.

” Duk wani da ake tunanin wani babu wanda bai kira ni ba irin su Abdullahi Abass…, Domin akan wannan abun saida cif joji ya kira ni mun yi zama da Cif Joji akan wannan ya kuma kira Alkali ya bashi Umarnin ya ci gaba da daure shi.

Idan ba a manta ba, har yanzu dai matashin dalibin nan dake karatu a Jami’ar Bayero dake Kano, Yahuza Tijjani na nan tsare a gidan kaso a dalilin wai ya yi rubutun suka ga wani dan majalisa dake wakiltar Madobi a majalisar jihar Kano.

Dan majalisar, Kabiru Ismaila ya zargi Yahuza da yin rubutun suka da cin fuska akan sa a shafinsa na Facebook.

Honarabul Ismaila bai yi wata-wata ba sai ya yi amfani da karfin kujerar sa ya sa ‘yan sanda suka cafke dalibi Yahuza.

Bayan yan kwanaki da yayi tsare a wurin ‘yan sanda sai aka kai shi kotun dake unguwar (No Mans Land) dake Karamar hukumar Fage, daga nan sai alkali ya daure Yahuza.

‘Yan uwan Yahuza da suka zanta da PREMIUM TIMES sun bayyana cewa suna kokarin ganin an sako Yahuza don ya koma makaranta amma abin ya citura domin ko daga baya da suka samu alkalin da ya yanke hukuncin tun a farko ya fadi musu cewa an maida shari’ar ofishin Antoni Janar din jihar.

” Mun yi ta jigila zuwa ma’aikatar shari’a ta jihar amma a duk sa’adda muka je sai a hana mu ganin kwamishinan. Babban abi da muke tsoro shine kada a sallameshi daga makaranta domin domin ya shafe tsawon lokaci baya zuwa karatu.

An ce Yahuza ya maida da martani ne ga wasu dake goyon bayan shi honorabul Ismaila a Facebook inda ya ce ” gwanin nasu ma bai iya lissafi ba sannan ko makaranta bai yi ba.” A tsakaninsu can a Facebook, amma shine wannan dan majalisar yayi amfani da dama da karfin kujerar sa ya a daure shi .

Kungiyar daliban Najeriya reshen jihar Kano sun yo tattaki bar zuwa ga wannan dan majalisa suka roke shi amma ya ki amincewa da ya bada da dama a sake shi.

PREMIUM TIMES ta samu ji daga bakin shi honorabul Kabir Ismaila, domin jin ko akwai dalilin da ya sa yaki sairaren jama’a da tausaya wa wannan dalibi.

” Yahuza ya ci mini mutunci ne ya. Da naga ba zan iya hakuri ko kuma in yi wani abu da zai saba wa doka ba sai na kai kara ga hukuma domin abi min hakki na. Amma babi wanda zai iya hakura da irin kalaman da wannan yayi a kai na.

Sakon barka da Jummah daga Sen.Ibrahim Shekarau Media

Kowane daya daga cikinku yaga barna, yayi kokarin canja ta da hannunsa, idan kuma bazai iya ba, to ya canja ta da harshen sa, idan kuma bazai iya ba, ya canja ta da zuciyar sa, ma’ana ya kyamace ta, amma wannan shine mafi raunin imani.

Muslim ne ya ruwaito wannan hadisi.

Barkan mu da Jummah

#SenIbrahimShekarauMedia

Yadda Ake Kokarin Haifar Da Rudani Tsakanin Buhari Da Osinbajo

Daga Rabiu Biyora:

Sakamakon tunkarar shekarar zabe ta 2023, wasu daga cikin al’umma sun fara aikin haifar da rudani tare da yinkurin saka shakku a cikin zukatan yan jam’iyyar APC akan kyakkyawar alakar dake tsakanin Shugaba Buhari da mataimakinsa Osinbajo.

A kwanakin nan sun fara ne da bayyana cewa wai shugaba Buhari ya ki bawa Osinbajo damar tafiyar da ayyuka bayan da shi Buharin yake gudanar da Private Visit a London, sun manta da cewa satin da ya wuce Mataimakin shugaban kasa ne ya jagoranci zaman majalisar zartarwa, kuma shine zai kara jagoranta a wannan rana ta Laraba.

A yanzu sai suke bayyana cewa wai Shugaba Buhari ya kori masu taimakawa Osinbajo har sama da talatin daga aiki, duk da cewa sun kasa kawo jerin sunayen wadanda aka dakatar tare da shaidar takardar dakatarwar, duk da cewa koda da gaske an dakatar din hakan ba zai zama yana da alaka da shugaba Buhari ba, sai dai a ce shi wanda suke yi wa aikin ne ya ga yiyuwar ya sauya su ds wasu, ballantana ma har zuwa yanzu babu kwafin takardar da za ta tabbatar da wannan ikirari.

Shirye-shiryen takarar zabukan 2023 za ta iya sanyawa a dinga jin bayanai kala-kala na fita, fata dai al’umma su nutsu kada su bari a yi yawo da hankalinsu.

#SenIbrahimShekarauMedia

Allah ya karawa rayuwa albarka Sardaunan Kano

Zan dauki wannan damar wajen yin godiya ga Allah da ya arzuta mu da shugaba na gari abin alfahari, dattijon fita kunya, wanda banyi nadamar kasancewa da shi ba, shugaba mai tsoron Allah mai yin umarni da kyakkyawa da hani da mummuna, shugaban da yake yafe wa duk wanda ya bata masa ko ya zalinceshi, haka kuma shugaban da yake yin umarni a yafe wa wada yayi kuskure, H. E. Sen. Ibrahim Shekarau CON (Sardaunan Kano)

A wannan rana 5 ga watan Nuwamba, 2019 ka cika shekaru 64 cikin bautawa Allah da kuma al’ummah, muna fatan Allah ya karawa rayuwa albarka, Allah ya baka mulkin Najeriya. Ameen.

#SenIbrahimShekarauMedia

KAI TSAYE DA SANATA SHEKARAU

A gobe Talata 5 ga watan Nuwamba 2019, Sanata Ibrahim Shekarau (APC-Kano Central) zai cika shekara 64 a duniya.

Haka a goben zai cika kwanakin aiki 100 cif da shiga zauren majalisar dattijai na Najeriya, yan shekara ta tara, wato 9th Session.

Da yardar Allah, Sanata Shekarau zai kasance da duk jama’a daga sassan duniya a shafukansa guda biyu na Face book a Shiri na Live Face Time. Duk mai son tambayar Sanata Shekarau ko bada wata gudunmawar shawara da hange zai iya ajiye tambayoyinsa da shawarinsa a yau da goben a wannan shafin. Za a tattara tambayoyin da gudunmawoyin da yardar Allah Sanata zai bada amsarsu kai tsaye ga duk masu kallo.

Wannan shiri zai zo da misalin karfe goma daidai na dare a goben. Zaka iya tambaya da Turanci ko da Hausa.

#SenIbrahimShekarauMedia

DAGA MAJALISAR DATTIJAI

Daga Jibril Muhammad Na Tara

Mai Girma Shugaban Kwamatin lura da harkokin aiki da duk Ma’aikata kuma Shugaban Kwamatin lura da walwalar Yan Fansho a Majalisar Dattijai Sanata Dakta. Malam Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta biya Yan Fansho bashin Naira Biliyan Dari Hudu ( N400bn)

Ya bukaci a fara biyan Yan Fansho kafin sauran Ma’aikata Kwamatinsa za su tsaya ka’in da na’in domin ganin Albashin Yan Fansho yayi dai – dai da sabon tsarin biyan Ma’aikata wanda Gwamnatin Tarayya ta ke Shirin aiwatarwa

yayi wannan furucin ne a yayin Zantawarsa ga manema Labarai (Team of Journalists) a wajen tantance Yan Fansho tare da sanya su a kan kwamfuta a Garin Lokoja dake Jihar Kogi a Ranar Juma’ah.
#VOICEOFSHEKARAU

#SenIbrahimShekarauMedia

DAGA MAJALISAR DATTIJAI

Daga Jibril Muhammad Na Tara

Mai Girma Shugaban Kwamatin lura da harkokin aiki da duk Ma’aikata kuma Shugaban Kwamatin lura da walwalar Yan Fansho a Majalisar Dattijai Sanata Dakta. Malam Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta biya Yan Fansho bashin Naira Biliyan Dari Hudu ( N400bn)

Ya bukaci a fara biyan Yan Fansho kafin sauran Ma’aikata Kwamatinsa za su tsaya ka’in da na’in domin ganin Albashin Yan Fansho yayi dai – dai da sabon tsarin biyan Ma’aikata wanda Gwamnatin Tarayya ta ke Shirin aiwatarwa

yayi wannan furucin ne a yayin Zantawarsa ga manema Labarai (Team of Journalists) a wajen tantance Yan Fansho tare da sanya su a kan kwamfuta a Garin Lokoja dake Jihar Kogi a Ranar Juma’ah.
#VOICEOFSHEKARAU

#SenIbrahimShekarauMedia

Allah ya yiwa Hon Inusa Ibrahim Dukurawa rasuwa

Daga Idris Gambo Wali:

Inna lillahi Wa’inna Ilaihir Raji’un!
Allah ya yiwa Hon Inusa Ibrahim Dukurawa tsohon shugaban karamar hukamar Dala, tsohon adviser a gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau rasuwa, anyi jana’jarsa kamar yadda addinin musulunci ya tanada, muna addu’ar Allah ya jikan sa yasa aljannace makomar sa, Allah ya farantar lahirar sa, Allah ya jikan al’umar Annabi Muhammad SAW. Ameen.

#SenIbrahimShekarauMedia

Sakon barka da Jumu’ah daga Sen Ibrahim Shekarau Media

Yaa ku wadanda kukayi Imani! Yayin da akayi kiran Sallah Jumu’ah, Kuyi gaggawar amsa kiran Allah domin sauraron bayanan addinin ku na musulinci wato Khutbah tare da yin Sallah.

Kuma ku rufe duk kasuwancin ku da duk wasu abubuwa da kuke yi, wannan shine ya fiye muku inda dai kun sani!

Barkanmu da Jumu’ah

#SenIbrahimShekarauMedia

Sakon Barka da Jummah daga Sen Ibrahim Shekarau Media

Wadannan da sukayi imani suka kyautata ayyuka kuma sukayi imani da abinda aka saukar wa Annabi Muhammadu (SAW) daga Ubangijin mu gaskiya ne, za’a shafe zunuban su kuma a daga darajar su.

Quran: Surah 47:2

Barkan mu da Jummah, Allah ya sada mu da dukkanin alkhairan da ke cikin ta, ya tsare mu daga dukkanin Sharrin da ke cikin ta.

KALAMAN WASU MUHIMMAN MUTANE KAN MAI GIRMA GWAMNA GANDUJE

DAGA Bashir Abdullahi El-bash

Yau Asabar, 12 ga watan Octoba, 2019.
Duba da yadda a kullum mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ke cigaba da samun yabo daga muhimman mutane kuma fitattu a ƙasa gaba ɗaya na ga dacewar na zaƙulo muku wasu daga cikin ɗumbin kyawawan kalaman yabo da jinjina da wasu daga cikin fitattun mutanen wannan ƙasa su ke furtawa game da shi a lokuta mabambanta domin girmama shi da kuma yaba kyawawan halayensa da salon yadda ya ke tafikar da gwamnati.

A wani lokaci da ya wuce baya a zamanin rayuwarsa, mai girma ɗan masanin Kano, Dakta Yusuf Mai Tama Sule, ya yi wa mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ƙirarin yabo da jinjina kala-kala. Daga ciki ya na cewa:

“Khadimul Islama Ganduje”, “Ganduje Gandun aiki”, “Ganduje ya san darajar mutane, ba ya cin mutuncin mutane, ba ya izgilanci, ba ya keta haddin ɗan adam”.

“Ni kuma ina tare da irin waɗannan mutane masu hali irin na Ganduje”. Inji mai girma ɗan masanin Kano, marigayi Dakta Yusuf Mai Tama Sule. Allah ya ji ƙansa ya yi masa gafara.

Haka zalika, shi ma tsohon ministan tsaron Nageriya, kuma tsohon shugaban rundunar sojin Nageriya, General Theophilus Y. Ɗan Juma, a ya yin wata ziyara da ya kawo Jihar Kano a wasu ƴan shekarun baya, ya yaba da kykkyawan salon tafikar da gwamnati irin na mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

A cikin jawabin da ya gabatar, T.Y Ɗan Juma ya yabawa gwamna Ganduje kan yadda ya ke ba da matuƙar kulawa wajen tsaftace Jihar Kano. Kamar yadda ya ke cewa: “A lokacin da na shiga mota daga filin sauka da tashin jiragen sama na tunawa da Marigayi Malam Aminu Kano zuwa gidan gwamnatin Jihar Kano, na ga Jihar Kano ta yi tsaf! Tsaf! duk inda na duba babu shara babu datti babu ƙazanta a kan titunan Jihar, ba shakka, wannan salo ne na shugabancin nagari irin na mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

Tabbas wannan abin yabo ne matuƙa, domin ƙazanta ce ta ke haifar da mafi yawan cututtukan da su ke yaɗo a cikin al’umma. Sai ga shi mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya na kula sosai da tsaftar muhalli a Jihar Kano.

A fannin ayyukan raya ƙasa ma, T.Y Ɗan Juma ya jinjinawa mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, kamar yadda ya ke cewa: “mun zagaya Jihar Kano, kuma idanuwanmu sun gane mana ɗumbin ayyukan cigaba, ba shakka gwamna Ganduje ya na aiki yadda ya kamata a Jihar Kano”.

Sannan kuma, T.Y Ɗan Juma ya kuma ƙara da yabawa mai girma gwamna kan yadda tsaro da zaman lafiya ke cigaba da samuwa a Jihar Kano, “Tsaro da zaman lafiya su ne jigon samar da duk wani cigaba ga kowacce irin al’umma a Duniya inji T.Y Ɗan Juma.

Daga nan kuma sai T.Y Ɗan Juma ya ƙarƙare da cewa, shugabanci irin na mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, abin sambarka ne matuƙa, domin shugabanci ne mai cike da aiki tuƙuru da juriya da kuma hangen nesa haɗi da kishin gina rayuwar al’umma”.

Haƙiƙa, wannan wani lamari ne da ke ƙara shaidawa duniya yadda manyan mutane masu kima da daraja su ka gamsu da nagarta da kyawawan halaye da ɗabi’un mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.

Idan mu ka yi duba da waɗannan mutane, za mu ga cewar dukkaninsu mutane ne gogaggu kuma fitattu waɗanda su ka san al’amuran mulki da al’umma, kuma masu nazari da bibiyar al’amuran yau da kullum ba ma a Nageriya kaɗai ba, har da sauran ƙasashen Duniya.

Fitar waɗannan kalamai daga bakunansu, ko shakka babu ƴar manuniya ce da ke tabbatar da nagarta da kuma kimar da mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ke da ita a cikin al’umma.

#SenIbrahimShekarauMedia

Auren shafin sada zumunta na facebook

Bayan rade-radin da al’ummar Najeriya suka yi ta yi har tsawon sati biyu cewa, shugaba Buhari zai daura aure da Hajiya Sadiya Umar Farouq kuma daya daga cikin ministocinsa a wannan rana ta Jummah.

Biyo bayan zargin da aka yi ta yi cewa, First lady Aisha Buhari, tayi yaji, bata dawo Najeriya ba tun bayan kammala aikin hajj a kasa mai tsarki a watan Agusta.

Masu sharhi daban-daban sunyi hasashen za’a daura wa Buharin sabon aure a yau Jummah, 11/10/2019 a babban masallacin Jummah na Abuja, inda dubban daruruwan jama’a suka tafi Abuja domin yin sallah a wannan masallaci ko Allah zai sa su shaida wannan daurin aure da aka yi hasashen daurawa a masallacin.

Amma kashhhh! Babu wata alama kuma ba’a daura wannan aure ba, daga nan kowa ya watse, maganar ta zama jita-jita ce kawai maras tushe ballantana makama a dandalin sada zumunta na facebook.

#SenIbrahimShekarauMedia

Kullun Nafsin Za’iqatul Maut

INNALILLAHI WA.INNA ILAIHIRAJIUWN
{Kullun Nafsin Za’iqatul Maut}

ALLAH YA YIWA YAR WAJEN AMINU ALI KABARA (FADIMATU ZAHRA.U) RASUWA

YAU ALHAMIS 10_10_2019
MUNA BARAR ADDU,AR KU ALLAH YA JIKANTA YAI MATA RAHAMA

A MADADIN SHUGABAN S4S ALH ABDULLAHI AHMAD TADADA MUNA ADDU’A ALLAH YAI MATA RAHAMA.

#SenIbrahimShekarauMedia

Shugaban Najeriya Buhari yana karanta kasafin kudin shekarar 2020

Shugaba Buhari ya gabatarwa da majalisun kasa kasafin kudin shekarar 2020 na Naira (#9.79trillion), inda ya gina kasafin kudin bisa dalar Amurika hamsin da bakwai ($57) akan farashin kowace gangar danyen mai.

Shugaban majalisar dattawa yasha alwashin majalisun zasu kammala aikin kasafin kudin da Buhari ke gabatarwa na shekarar 2020 kafin karshen wannan wata na October.

Allah ya taimaki Najeriya.

#SenIbrahimShekarauMedia

GODIYA MUKEYI KAROTA.

Daga Bello Aliyu:

DOTSA DA DANGORO UNGUWANNI NE DAKE AKAN TITIN ZARIA KUMA DUK MAI MOTA, DRIVER KO FASINJA YASAN HATSARIN DAYAKE FUSKANTA DA ZARAR YAZO WAJEN SABODA YANDA YAN TIRELOLI DA SAURANSU SUKEYIN FAKIN NA GADARA DA GANGANCI, WALLAHI DUK MAIBIN HANYAR NAN MUSAMMAN DA YAMMA YASAN MENAKE NUFI. TO CIKIN IKON ALLAH KAROTA SUNKAWO MANA KARSHEN FAKIN ANAN WAJEN. DAGA JIYA ZUWA YAU DUK WANDA YABIYO HANYAR ZAISHA MAMAKI. HOTON DA ZAKU GANI AKASAN RUBUTU NA NADAUKESHI DA SAFIYAR YAU AKAN HANYATA TA TAFIYA AIKI KARFE 6:30.
KAROTA AKARA TAUSAYI DA KULAWA AKAN AIKI. ALLAH YAYI MANA JAGORANCI.

#SenIbrahimShekarauMedia

Yadda Gwamna Ganduje Ya Binne Abba, PDP, Da Kuma Kwankwaso A Siyasa

SHARHI NA MUSAMMAN

DAGA Bashir Abdullahi El-bash:

-Nasarar Gwamna Ganduje A Kotu, Nasarar Dimokaraɗiyya Ce, Inji Shugaba Buhari

-Ta Tabbata Gaskiya Ta Yi Halinta, Kotu Ta Tabbatarwa Jama’ar Jihar Kano Abin Da Su Ka Zaɓa Da Hannayensu, Inji Gwamna Ganduje

-Ɗaukaka Ƙara Da PDP Da Abba Gida-Gida Da Kwankwasiyya Su Ka Yi, Tamkar Ɓata Kuɗi Da Lokacinsu Za Suyi, Cewar Tsohon Kwamishina, Muhammad Garba.

Yau Talata, 8 ga watan Octoba, 2019.
Ranar Laraba, 2 ga watan Octoba, 2019, rana ce wacce ta kasance ta farin ciki da murna ba ga mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje kaɗai ba, har da ɗaukacin al’umma masoya da kuma masu yi wa Jihar Kano fatan alkhairi.

Tun bayan da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta ayyana mai girma gwamna, Dakta Abdullahi Umar Ganduje a matsayin wanda ya lashe zaɓen ranar 23 ga watan Maris, 2019, al’ummar Jihar Kano su ka samu nutsuwa da kwanciyar hankali, saboda sun gamsu zaɓen ya gudana cikin nasara da lumana.

A wannan rana, al’umma sun gudanar da bukukuwa da shagulgulan murnar wannan nasara da mai girma gwamna ya samu a dukkan loko da saƙo na ƙananan hukumomin Jihar Kano (44) kowa ya ji a ransa cewar wannan nasara tasa ce.

Amma abin mamaki, sai ga jam’iyyar (PDP) da ɗan takararta na gwamna Abba Kabir Yusuf (Abba Gida-Gida) da kuma rusasshiyar ƙungiyar nan ta Kwankwasiyya sun yanke shawarar ƙalubalantar wannan nasarar da mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya samu a kotun sauraren ƙararrakin zaɓen gwamna

Abba Kabir, bisa jagorancin mai gidansa, Rabi’u Musa Kwankwaso, sun tattara hujjojin da ba su inganta ba sun miƙawa manyan lauyoyinsu, waɗanda su da kansu sun riga sun san cewar sun ɗauki dakon shari’ar da ba nasara za su samo ba.

Bayan shafe tsawon watanni uku lauyoyi su na fafutukar sauya haƙiƙanin al’amuran da su ka faru tare da gabatar da hujjoji masu rikitarwa waɗanda ba su inganta ba.

Lauyoyin mai girma gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje da na hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC), haɗe da na jam’iyyar (APC), cikin nutsuwa da bin ƙa’ida sun kare shari’ar tare da gabatar da sahihan hujjojin da su ka rusa dukkan zarge-zarge marasa hujja da masu ƙara su ka gabatar a gaban kotun.

Kamar yadda aka tsammata, a ranar yanke hukuncin ƙarshe, mai shari’ar da ta jagorancin zaman yanke hukuncin, mai shari’a Halima Shamaki, bayan shafe tsawon awanni uku ta na gabatar da bayanai, daga ƙarshe ta yi watsi da ƙarar da jam’iyyar (PDP) ta shigar ta na ƙalubalantar nasarar da gwamna Ganduje ya samu a zaɓen 9 da 23 ga watan Maris ɗin shekarar (2019).

Kotun ɗaukaka ƙarar ta bayyana rashin hujjoji gamsassu daga masu ƙara (PDP) a matsayin dalilan da su ka sanya ta yi watsi da ƙarar da su ka shigar su na ƙalubalantar nasarar ta gwamna Ganduje a zaɓen gwamna na shekarar (2019).

Kotun ɗaukaka ƙarar ta kuma ƙara da bayanin cewa soke sakamakon zaɓukan Mazaɓar Gama da na wasu Mazaɓu da aka yi su ka kuma haifar da sake maimaita zaɓen cike giɓi, ba wai batu ba ne na doka kawai, zaɓen ya zama karɓaɓɓe.

Mai shari’a Shamaki ta kuma ƙara da cewa, “Bambancin shi ne akwai ƙuri’un da ake nema a mazaɓar gama guda (128,000) idan aka haɗa su da ƙuri’u (26,000) na ɗan takarar jam’iyyar (PDP) Abba Kabir Yusuf. Dan haka akwai buƙatar a gudanar da wannan zaɓe zagaye na biyu na ranar 23 ga watan Maris, 2019 domin kammala zaɓe gaba ɗaya.

Sai kuma mai shari’a Shamaki ta ƙara da shaida cewa, matakin da hukumar zaɓe ta (INEC) ta ɗauka na bayyana zaɓen 9 ga maris a matsayin wanda bai kammala ba, da kuma sake shirya zaɓen cike giɓi da ta yi, ya yi daidai matakin ya na kan turbar doka da ƙa’ida cikin kundin tsarin mulkin ƙasa da tanade-tanaden dokokin zaɓe.

Sannan kuma ta ƙara da tabbatar da cewa masu ƙara ba su iya gabatar da hujjoji gamsassu ba.

Daga nan kuma mai shari’a Halima Shamaki ta ƙara da cewa matakin sake zaɓe ba wai na iya hukumar zaɓe ta (INEC) ba ne, hatta su kansu jam’iyyun siyasa ciki har da jam’iyyar da ta kawo ƙarar, duk sun gamsu da matakin gudanar da zaɓen na cike giɓin.

Tun bayan da labari ya bazu cewar kotu ta yi watsi da wannan shari’a, al’ummar Jihar Kano su ka bazama kan tituna cikin shauƙi da murnar wannan nasara, wanda hakan ke nuni da kotu ta tabbatar da abin da su ka riga su ka sani, hukunci na gaskya.

Wannan shi ne yadda gwamna Ganduje, cikin shara ɗaya ya binne Abba Kabir Yusuf da jam’iyyar (PDP) da ƙungiyar Kwankwasiyya a kabarin da ke cikin maƙabartar siyasa, abin da ba su taɓa tunanin fuskanta ba.

Cikin jawabinsa jim kaɗan da bayyana sakamakon hukuncin kotun, gwamna Ganduje ya bayyana cewa “gaskiya ce ta yi halinta”

“A lokacin da aka gudanar da wannan zaɓe mun samu nasara, amma jam’iyyar adawa ta (PDP) ta ƙalubalanci wannan nasara da mu ka samu zuwa kotun shari’un ƙararrakin zaɓe. Sai dai kuma, yanzu ta bayyana a fili ga kowa nasarar tamu ce, kotun ta tabbatar da hakan”.

Daga nan kuma sai gwamna Ganduje, ya ba da tabbacin samar da adalci ba tare da nuna wariya ko wani bambancin ga kowa ba. Kamar inda ya ke cewa:

“Ni gwamna ne na kowa ba tare da nuna bambanci ba, kamar yadda hakan ke ƙunshe cikin manyan manufofin jam’iyyarmu ta (APC)”. Inji Gwamna Ganduje.

Sai kuma ya cigaba da ba da tabbacin yin tafiya da kowa cikin buɗaɗɗiyar gwamnati kamar yadda ya faro a zangon mulkinsa na farko, “zan cigaba da yin aiki tuƙuru cikin juriya da sadaukarwa domin kyautata rayuwar al’ummata a wannan Jiha tamu abar alfaharinmu”. Inji Gwamna Ganduje.

A ƙarshe kuma sai gwamna Ganduje ya sake jaddada saƙon godiyarsa ga al’ummar Jihar Kano da su ka sake zaɓarsa a zangon mulki na biyu, sannan kuma su ka cigaba da yi masa addu’a kan ƙalubalantar nasararsa da ƴan adawa su ka yi a kotu, har zuwa wannan lokaci da Allah ya ba shi wannan nasara a kotun.

“Yau rana ce ta murna da farin ciki, ya yin da kotun sauraren ƙararrakin zaɓe ta tabbatar mana da nasarar da Allah ya ba mu a sanadiyyar zaɓen da al’umma su ka yi mana tun a baya”. Inji Gwamna Ganduje.

“Wannan nasara ce ga dimokaraɗiyya’ -Inji Shugaban Nageriya, Muhammadu Buhari.

A saƙon taya murna da ya aike, shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana nasarar gwamna Ganduje a matsayin nasara ga dimokaraɗiyya.

Shugaban na Nageriya, ya bayyana yadda shari’ar ta gudana a matsayin nasara ga dimokaraɗiyya. Tare da godewa al’ummar Jihar Kano kan yadda su ka martaba zaman lafiya, su ka bi hanyoyin shari’a kamar yadda doka ta tanadar a dimokaraɗiyya.

Dangane da abubuwan da su ka faru a daga zaɓe da kuma hukuncin kotu, shugaba Muhammadu Buhari ya hori gwamna Ganduje kan cigaba da samar da haɗin kai a Jihar Kano domin tunkarar cimma ƙudurorin jam’iyyar (APC) na kyautata rayuwa da samar da walwala ga al’umma. Shugaba Buhari ya faɗi haka ne ta cikin wata sanarwa da ya fitar ta hannun babban jami’insa na musamman kan harkokin watsa labarai, Mallam Garba Shehu.

“Kada ku ɓata ƙarfi da kuɗaɗenku, shawarar Muhammad Garba ga jam’iyyar (PDP).

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai, Mallam Muhammad Garba, ya shawarci jam’iyyar (PDP) da ɗan takararta na gwamna, Abba Kabir Yusuf da su rungumi ƙaddara su janye ƙudurinsu na sake ɗaukaka ƙara a kotu ta gaba

Muhammad Garba da ya ke jawabi la’akari da zaman lafiya da kuma cigaba gami da yadda yadda siyasar Jihar Kano ta kai matakin cikar nagarta, ya buƙaci Abba Kabir yusuf da ya rungumi shan kaye cikin girma da daraja.

Ya bayyana cewa, la’akari da yadda kotun ta gudanar da saurare game da yanke hukunci kan shari’ar, (PDP) ba ta iya gabatar da hujjoji gamsassu kan zargin da ta ke yi ba.

Muhammad Garba ya kuma nazarci cewa, jam’iyyar (PDP) da ɗan takararta, babu wata shari’a da za su ɗaukaka ƙara akai duba da yadda su ka gabatarwa da kotun farko raunanan hujjojin da ba su inganta ba kan zargin ba daidai ba da su ke tunanin an yi a ya yin zaɓen gwamna.

Daga nan kuma sai tsohon kwamishinan ya buƙaci al’ummar Jihar Kano musamman ma magoya bayan jam’iyyar (APC) da su cigaba da kasancewa cikin kwanciyar hankali da lumana, ka da su yarda su sanya kansu cikin duk wata tarzoma domin jami’an tsaro ba za su lamuci karya doka da rusa zaman lafiya a Jihar Kano ba.

Bikin cikar Nageriya shekaru (59) da samun ƴancin kai, gwamna Ganduje ya buƙaci kauda bambance-bambancen da ke tsakani domin ciyar da ƙasa gaba.

Gabanin shagulgulan murnar samun nasara a kotu, albarkacin cikar Nageriya shekaru (59) da karɓar ƴancin kai daga turawan mulkin mallaka na Ingila, gwamna Ganduje ya buƙaci dukkan ƙabilun da ke Jihar Kano da su kauda bambance-bambancen da ke tsakaninsu domin ɗorewar zaman lafiya da kuma haɗin kai da Jihar gaba.

Gwamna Ganduje ya bayyana haka ne a filin wasa na tunawa da marigayi Janar Sani Abacha da ke Ƙofar Mata, tare da jan hankali kan batun haɗin kan ƙasa a madadin rarrabuwa.

“Bambance-Bambancen da ke tsakaninmu ta fuskar al’adu da kamance, ka da ya zama abin da zai haifar mana da rarrabuwa, mu fahimci bambance-bambancen domin mu zauna lafiya cikin girmama juna”.

Gwamna Ganduje wanda mataimakinsa, Dakta Nasiru Yuauf Gawuna ya wakilta, ya bayyana taken taron na bana da “zaman lafiya kan haɗin kai da gina ƙasa” duba da matsalolin hantara da ƙyamar juna gami da nuna bambance-bambancen yanki da shiyya da rashin zaman lafiya a tsakankanin al’ummun yankunan wannan ƙasa.

Sannan kuma gwamna Ganduje ya yi tsokaci kan batun cigaba da wayar da kan matasa dangane da kyawawan halaye da ɗabi’u kan batun zaman lafiya da haɗin kai domin samar da cigaba mai ma’ana a Jiha da kuma ƙasa gaba ɗaya. Kamar inda ya ke cewa:

“Matasanmu jari ne mai girma a tattare da mu, mun yi imani cewa ƙaddararsu ba wai ta na nufin matsayinsu kenan ba a rayuwa, a matsayinmu na iyaye ko gwamnati, ko al’umma, ba za mu zuba ido mu ƙyale su kara zube ba, za mu cigaba yi musu uzuri da ƙoƙarin ganin sun fita daga cikin mawuyacin halin da su ke ciki domin samun kykkyawar rayuwa”.

Wannan gwamnatin tamu, ta tallafawa matasa sama da mutum (200,000) a zangon mulkin farko, kuma za mu cigaba da ganin mun daƙile matsalolin da matasanmu su ke fuskanta a wannan Jiha.

Gwamna Ganduje ya kuma cigaba da cewa, a cikin shekaru huɗu da su ka gabata, gwamnatinsa ta samu nasarar cimma managartan nasarori a fannin ilimi da na lafiya da na tsaro da na noma da kuma manyan ayyukan raya Jiha da samar da ayyukan yi. Kuma a yanzu ma a wannan zango na biyu za ta ɗora daga inda ta tsaya ne domin cigaba da samar da ƙarin ɗumbin nasarori.

“Mun yi dogaro da cewa hanya mafi a’ala ta samar da ilimi ga waɗanda su ka cancanta ita ce ta ba da ilimi kyauta, kuma mun bayyana ƙudurinmu na fara bayar da ilimi kyauta tun saga firamare har zuwa babbar sakandire, kuma kowa ya gani a cikin watan da ya gabata mun fara aiwatarwa.

“Ina mai farin cikin tabbatar muku cewa, za mu cigaba da kyautata makarantunmu na gwamnati tare da tabbatar da cewar yaranmu sun samu horo mai inganci. Za kuma mu cigaba da horar da malaman hanyoyi da dabarun koyarwa irin na zamani domin samun kykkyawan sakamako cikin ajujuwa.

A fannin ƙoƙarin gwamnati wajen inganta sashen lafiya kuwa, gwamna Ganduje ya bayyana cewa fannin lafiya a Jihar Kano ya karɓi manyan nasarori a cikin shekaru huɗu da su ka gabata, inda gwamnati ta kammala aikin ginin asibitin Mallam Isyaka Rabi’u da Kuma Muhammad Buhari Specialist Hospital gami da sabuntawa da kuma ɗaga darajar wasu asibitocin tare kuma da samar musu da kayan aiki irin na zamani da kuma samar ƙarin cibiyoyin lafiya sama da guda (300) a sassa daban-daban na Jihar Kano.

Gwamna Ganduje ya kuma ƙara da cewa akwai tsare-tsare na cigaba da samar da ayyukan raya jiha a dukkan birane da karkara inda za a cigaba da samar da tituna da gadojin sama da na ƙasa domin kyautata harkokin sufuri ga al’umma da kuma bunƙasa tattalin arziƙin Jiha.

Sauran fannonin da gwamnatin gwamna Ganduje ta samu nasarar cimma managartan nasarori har da batun samar da wadataccen abinci a Jiha da kuma daƙile matsalar rikicin fulani makiyaya da manoma matsalar da ke barazana ga harkar tsaro da batun zaman lafiyar ƙasa. daƙile matsalar rikicin fulani makiyaya da manoma, matsalar da ke barazana ga harkar tsaro da batun zaman lafiyar ƙasa.

#SenIbrahimShekarauMedia

KUNE KUKA BATA RARARA

Daga Umar Faruq Muhammad:

Dauda Adamu Abdullahi Kahutu Rarara yayi shuhura a wakokin Siyasa ne a lokacin Mulkin Sardaunan Kano Mal. Ibrahim Shekarau, haka nan wakokin sa sunyi tasiri sosai tare da dadi irin wanda ake bukata.

Duk wanda yasaurari wakokin Rarara na wancan lokacin irin su SARAKI SAI ALLAH zaiji cewa zallar Yabo ne ga Dan siyasar dayake so, hakanan a fannin suka ga abokin Hamayya yanayi cikin hikima da Mutunci babu batun cin fuska.

Ko a lokacin da aka samu sabanin ra’ayin siyasa wajen takarar 2011 Dauda yayi wakoki ga tsagin dayake goyawa baya, saboda tarbiyyar siyasar dayake da ita a lokacin babu cin Mutunci ko bayanannen keta haddi ga wadanda yakewa hamayya.

Tarbiyyar wakokin Rarara ta zube ne a sanda ya narke cikin Gwamnatin 2011, dayake yaji irin sunayen da Mutanen Gwamnatin ke kiran tsohon Gwamna irin su Duna tuni yafara amfani dasu don yafaranta musu, sukuma suka dinga zugashi ta hanyar yayyafin kudi da tafi da sowa.

Sada Bin Suleiman Usman da Anas Darazo kunji daga inda aka samo saudewar hanyar?!

#SenIbrahimShekarauMedia

Kotu ta kara tabbatar da gwamnan Bauchi

Kotun sauraron kararrakin zaben gwamna a Jihar Bauchi ta tabbatar da gwamna Muhammed Abdullahi Abubakar a matsayin halattaccan wanda ya lashe zaben.

#SenIbrahimShekarauMedia

ZARGIN DA AKE YIWA WASU SOJOJI AKAN ALAKA DA KUNGIYAR BOKO HARAM

Daga Datti Assalafiy:

Nayi bincike daga tushe, kuma na samu tabbacin cewa rundinar sojin Nigeria tana neman wasu sojojinta guda 22 ana zarginsu da cin amana wajen taimakon ‘yan ta’addan Boko Haram da bayanan sirri

Ga jerin sunayen sojojin da ake nema ruwa a jallo kamar haka:
1- Major Mallam Turaki
2- Major U.A. Nagogo
3- Staff Sergeant Benjamin Afolabi,
4- Sergeant Christian Nwachukwu,
5- Sergeant Patrick Kosin
6- Sergeant Awuwa Orin
7- Sergeant Ibrahim Amodu
8- Sergeant Nasiru Umar
9- Sergeant Bello Suleiman
10- Sergeant Josiah Seth
11- Sergeant Muazu Nura
12- Sergeant Ayodeji Ogunsuji
13- Corporal Michael Friday
14- Corporal Wakili Saul
15- Corporal Akyen Zamani
16- Corporal Yahaya Abubakar-Doia
17- Lance Corporal Isikuru Venture
18- Lance Corporal Aminu Isiaku,
19] Lance corporal Usman Suleiman
20- Lance Corporal Maigari Markus
21- Lance Corporal Edward Ofem
22- Lance Corporal Adams Shehu.

Muna rokon Allah Ya tona musu asiri a duk inda suka buya idan ya tabbata maciya amana ne, idan ba su da laifi Allah Ya basu mafita

#SenIbrahimShekarauMedia

KIRISTOCI SUN HANA MU SHIGA WANI KAUYE A JIHAR KANO JIHAR MUSULMI!!!

Daga Musa Muhammad Idris Dankwano.
29-08-2019.

WANI ABIN TAKAICI DA YA SAME MU A YAU!!!

A yau Lahadi 29-09-2019 mu ka shirya fita Da’awar addinin musulunci zuwa wani gari da ake kira “Faala” a cikin karamar hukumar Tudun Wada a Jihar Kano Arewacin Nigeria, inda daga nan kuma zamu gangara mu shiga wani Lungu da ake kira da “Bangaa” a dai Karamar Hukumar Tudun Wada Jihar Kano domin dubiyar wani Musulmi maras lafiya da ke cikin wannan Kauye na “Bangaa”. Da kuma isar da sakon musulunci idan dama ta samu.

Garin Faala karamin kauye ne dake dauke da al’umma sama da dubu, kuma dukkan su Musulmi ne babu Kirista ko Bamaguje ko Mutum daya. Har ma suna da Katon masallacin Juma’a.

Tafiyar Mintuna talatin (30) ne ko kusa da haka a tsakanin garin Faala da kuma wani karamin Kauye mai suna “Bangaa” wanda ke karkashin dagacin Faala.

Shi wannan karamin kauye mai suna “Bangaa” baki dayan garin Kiristoci ne, in banda Mutum biyu (2) ko uku (3)

Bayan mun isa garin Faala a yau Lahadi 29- Sept. 2019,mun shiga fadar Mai girma Dagacin garin mun yi gaisuwa a gare shi ta ban girma, mun kuma sake neman izini a gare shi, duk da cewa mun aika masa sakon zuwan mu da kuma neman izinin gabatar da wa’azin musulunci a yankinsa. Kuma ya amince ya bamu goyon baya kamar dai yadda doka ta tanada.

Bayan gaisa da Mai girma dagaci, mun nemi ya hada mu da wakili wanda zai yi mana jagora domin shiga kauyen Bangaa, kauyen da baki dayansa kiristoci ne in banda mutum biyu ko uku da suke musulmai, inda Dagaci ya hada mu da da’nsa na cikinsa wanda shima yana da sarautar mai unguwa,Mai Unguwa yayi mana jagora muka hau mota tare dashi domin isa zuwa ga kauyen Bangaa, muyi dubiyar maras lafiya,sannan muyi amfani da dama idan ta samu muyi kira zuwa ga addinin Islam.

Mun kama hanya mun durfafi kauyen Bangaa, wanda da kyar mota ke iya shiga saboda ramuka da kwazazzabai da ciyayi da itatuwa, kwatsam!!! Bayan mun yi tafiya ta kimanin mintuna ashirin a cikin jeji, muna daf da shiga kauyen!!! Sai ga dandazon matasa majiya karfi kimanin mutum (7) sun tare hanya sun gindaya baburansu.

A nan Matasan nan suka tsayar da mu, suka ce bamu isa mun shiga kauyen su ba. Idan kuma muka shiga to sai dai iyayen mu su haifi wasu. Suna zagin mu, suna yi mana barazana iri-iri, mu kuma muna lallashin su da basu hakuri, inda a karshe duba da wasu dalilai na maslaha da gudun fitina muna ji muna gani muka hakura muka juyo cikin rashin jin dadi.

Matasan sun fito ne daga kauyen bisa umarnin Shugaban su (Pastor) wanda asalinsa dan jihar Katsina ne,ba ma Dan Jihar Kano bane!!! Kawai Kungiyar kiristoci ce ta dauko shi ta kawo shi wannan kungurmin lungun domin yana jagorantar cocinsu.

Ko a waccan shekarar mutanen mu sun shiga garin Bangaa da nufin su gaisawa da shi don su fahimci juna, amma suna shiga yasa aka debo makamai aka koro su.

To yau ma sai ga shi ya sake bayar da umarni, yace mabiyansa kada su sake su bari mu shiga masa gari. (Kai kaji rashin kunya da raini wai garinsa, alhali akwai mai unguwa akwai dagaci da ke da iko da kauyen)

Haka nan shi Mai Unguwa da aka hada mu dashi a idonsa komai ya faru, yayi ta kokarin basu baki, yayi magiya, yayi lallashin, amma suna dukan kirjinsa suna zage-zage da ashariya suna nuna mu da yatsu cewa mu janye motocin mu, kada mu sake mu shigar musu kauye!!! Sun bamu dan lokaci mu bar wajen ma da suka dakatar da mu ko kuma duk abinda suka yi mana ba ruwansu!!!

Mai Unguwa dai ya sake bamu labari cewa, shi wannan Pastor shugaban cocin kauyen Baaga wanda Mutumin Katsina ne, kwanaki yazo har cikin gidan Dagaci yana masa kashedi da cewa ya daina bari musulmi suna shiga masa gari fa!!!.

Yan uwa masu karatu wannan fa dambarwa ta faru ne a cikin Jihar Kano ba a Enugu, ko Onitsha, ko wani gari cikin manyan garuruwan kiristoci a Nigeria ba!! A’a a jihar Kano!!!

Wanda mun san a tsarin dokar kasa babu wani farar hula da ya isa ya hana wasu shiga wani waje, babu wanda ya ke da ikon hana wasu yin kira zuwa ga kowanne addini.

Amma sai gashi abun takaici Pastor ya hana Musulmi Yan cikin Jihar Kano, kuma har ma da Yan karamar hukumar, kai har ma da mai sarautar gargajiya shiga wani kauye domin suyi dubiyar maras lafiya su kuma yi da’awar addininsu.

Hakika wannan raini ne!!! Wannan cin kashi ne!!! Wannan sakaci ne na musulman Jihar Kano da har muka bari aka shigo aka raina mu haka.

(1) Mun sanar da wannan abu ne da ya faru domin mu janyo hankulan Y’an uwan mu Musulmi, su sani cewa muna gidajen mu muna sharar bacci kiristoci suna aiki ba dare ba rana, sunyi amfani da damammakinsu sun shiga kauyuka da lunguna sun yi karfi sun kuma cusa kiyayya a zukatan mutanen kauyen akan Yan uwan su a harshe da al’ada da jinsi.

(2) Wajibi ne zamu dauki matakin da ya dace na shari’a bisa yadda doka ta tanada akan wannan Pastor da yayi mana barazana ya kuma tauye mana hakkokin mu.

(3) Muna kira ga dukkan al’ummar musulmin Jihar Kano da ma kewaye, su sani akwai aiki a gaban mu matuka. Wallahi idan ka shiga lungunan wasu kananan hukumomin Kano,kamar: Tudun Wada,Sumaila,Garko da makamantansu zaka sha mamaki na irin barnar da kiristoci su kayi a wadannan wurare! Domin yau Lahadi mun ga abubuwan takaici a kan hanyar mu. Saboda haka ya zama wajibi mu farka daga baccin da mu ke yi! Mu tashi da gaske mu taimaki wannan addini namu na gaskiya.

Allah Ya sauwaka Allah Ya sa mu dace.

#SenIbrahimShekarauMedia

Najeriya59

Cikakken dan kishin kasa kuma tsohon shugaban gwamnatin soja a Najeriya Janar Yakubu Gowon (mai ritaya) ya halarci bikin cikar Najeriya shekaru hamsin da tara (59) da samun mulkin kai.

Allah ya taimaki Najeriya da masu kishinta, yasa mu fita daga kangin da wadancan shugabannin suka jefa al’umma wanda har zuwa yanzu yake bibiyarmu.

#SenIbrahimShekarauMedia

Design a site like this with WordPress.com
Get started