Za abi doka domin dakatar da asusun hadin gwuiwar kananan hukumomi da jihohi

Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha yasha alwashin kawo karshen asusun ajiyar kudade na hadin gwuiwa tsakanin gwamnatocin kananan hukumomi da gwamnatocin jihohi ta sahihiyar hanyar amfani da tsarin mulkin Najeriya.

Boss Mustapha yace, wannan hadakar asusun ajiyar kudade ana amfani dashi ta hanyar da bata dace ba, don haka ya zama wajibi a dakatar dashi domin sakarwa gwamnatocin kananan hukumomi mara su sami damar yin fitsari.

#SenIbrahimShekarauMedia

Najeriya: Fusatattun matasa sunkai farmaki ofishin MTN

Wasu fusatattun marasa a Jihar Lagas da Ibadan a Jihar Oyo sun kai farmaki a kantin Shop rite da ofisoshin MTN sakamakon yadda ‘yan kasar Afrika ta Kudu suke kashe ‘yan Najeriya a can Kasar tasu.

Suma wadannan kamfaninnika na Shop rite da MTN mallakin mutanen Kasar Afrika ta Kudu ne, shine nan take matasan suka kai musu farmaki domin ramuwar gayya.

Tuni Shugaban Kasa Buhari ya gayyaci mataimakinsa da ministan cikin gida domin tattaunawa ta gaggawa yadda za’a shawo kan lamarin, a gefe guda kuma labarin da muka samu na cewa, Gwamnatin Najeriya ta umarci wakilinta a Kasar Afrika ta Kudu yayi gaggawar dawowa gida Najeriya.

#SenIbrahimShekarauMedia

FEMI FANI KAYODE YA LA’ANCI SHUGABA BUHARI

Daga Datti Assalafiy:

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama, kuma babban jigo a cikin jam’iyyar PDP Femi Fani Kayode babban makiyin arewa da musulunci ya la’anci Maigirma shugaban Kasarmu Nigeria Muhammadu Buhari sakamon abinda yake faruwa a Kasar Afirka ta kudu.

Wani irin bakar kiyayya ne haka?
Menene laifin shugaba Buhari akan ta’addancin da mutanen Afirka ta kudu suke yiwa ‘inyamurai ‘yan Nigeria mazauna Kasar har ya cancanci tsinuwa daga wannan makiyi namu?

A daidai lokacin da dukkan ‘yan Nigeria suka hadai kai, suka kawar da banbancin akida, addini, yare, kabila da yanki suka fito suna Allah wadai da abinda ake yiwa inyamurai ‘yan Nigeria a Kasar Afirka ta kudu shi kuma Femi Fani Kayode a daidai wannan lokacin ya fito yana kokari tarwatsa wannan hadin kan.

Na sha fada ba sau daya ba, kuma ba sau biyu ba; Femi Fani Kayode ‘dan kwangilar tarwatsa Nigeria ne, makiyin Nigeria ne, tsinanne ne, hatsarinsa daidai yake da hatsarin shugabannin kungiyoyin ta’addanci da suke da burin tarwasa Nigeria, ganganci ne gwamnatin Nigeria ta zuba masa ido yana yin abinda yaga dama.

Kuma abinda Femi Fani Kayode yake yi na yiwa arewa da Musulunci batanci da sunan siyasa ni dai yana kara min tsanar jam’iyyar sa ta PDP, babu abinda zai karawa jam’iyyarsa na PDP face bakin jini da kiyayya, ya kamata shugabannin jam’iyyar PDP su gane wannan mutumi hatsari ne a cikin jam’iyyar su.

Ubangiji Allah kamar yadda Femi Fani Kayode ya la’anci shugaba Buhari Allah Ka mayar da la’antar kanshi, Allah Ka shafe tasirinsa a cikin Kasarmu Nigeria.

#SenIbrahimShekarauMedia

Janar Bashir Salihi Magashi

Daga Bello Muhammad Sharada:

SABON MINISTAN HARKOKIN TSARO

Jiya Asabat kungiyar masu kishin ci gaban jihar Kano KCCI suka shirya taron karrama sabon ministan harkokin tsaro na kasa Janar Bashir Salihi Magashi. A wajen maida martanin jawabansa ne ya gaya wa jama’a cewa shugaban kasa Muhammad Buhari ya yi barcinsa da minshari, ya sha kuruminsa, zasu yi aiki kuma lamarin tsaron kasar nan zasu kawo shi karshe kuma yana wuyansu duk wata gaza wa a tuhume su kuma a zargesu.

A BISA LISSAFI duk manyan kusoshi da suke rike da madafun tsaro na kasar nan suna hannun arewa, in banda ministan harkokin cikin gida, sannan kuma matsalar a arewa tafi kamari.

GA WADANDA TSARO KE HANNUNSU

Commander In Chief PMB
Ministan tsaro Kano Janar Magashi
NSA: Borno Muhammad Munguno
IG Police Nassarawa Muhammad Adam
Chief of Army Staff Borno Yusuf Burutai
Chief of Air Staff Bauchi Sadique Abubkr
DSS Kano Yusuf Magaji Bichi
NIA Katsina Ahmed Rufai Abubakar
Nigeria Civil Defense Niger Abdullahi Gana
Ministan Police Maigari Dingyadi
Ministan Cikin Gida AbdurUf Aregbesola
CG Custom Bauchi Hamid Ali
CG Immigration Jigawa Muh Babendede
CG Prisons Kebbi Jaafaru Ahmed
Chief of Staff Borno Abba Kyari
SGF Adamawa Boss Gidi Mustapha

A tsakanin watan Janairu 2019 zuwa wannan watan da ya shude na July 2019, Madam Amina Shamaki, Babbar sakatariya a ofishin sakataren gwamnatin tarayya mai lura da Ayyuka Na Musamman ta ce an kashe mutum 1460, a Najeriya, ma’ana duk watan duniya tun daga Janairu har zuwa Yuli sai an kashe mutane 210. A tsakanin wannan watanni bakwai kuma sau 330 aka kai farmaki.

Wannan fa ku cire duk wani lissafi da watan Agusta har da wanda ya faru a WURMA ta Katsina.

A wannan watanni bakwai “Nigerian Security Tracker” ta jero

JIHOHIN DA AKA FI GARKUWA DA MUTANE

1. ZAMFARA 146
2. RIVERS. 126
3. KADUNA. 124
4. KATSINA. 100
5. NIGER. 79
6. KOGI. 34
7. BORNO. 34
8. EDO. 33
9. TARABA. 24
10.AKWA IBOM 20
11.ONDO. 17
12.SOKOTO. 16
13.BAYELSA. 12
14. OGUN. 11
15. NASSARAWA 10
16. FCT. 9
17. OSUN. 8
18. LAGOS. 8

DARASI: Wannan kididdiga ta nuna kwata-kwata an daina Garkuwa da mutane a jihohin Inyamurai na SouthEast wato daga inda musiba ta taso, an dawo jihohin Hausa Fulani a North West da duk arewa da Niger Delta da yankin Yarbawa.

TUNDA JANAR MAGASHI YA CE YA JI YA GANI, MUN BASHI KWANA 120 MU GA KAMUN LUDAYINSA. ZAMU RIKA YI MASA ADDU’A KUMA MUNA TUNATAR DA SHI

#SenIbrahimShekarauMedia

Cross River: ‘Yan sanda sun kame wani dan jarida

‘Yan sanda a Jihar Cross River sun kame wani dan jarida Agba Jalingo, saboda yayi zargin Gwamnan Jihar Professor Ben Ayade da karkatar da kudade har Naira miliyan dari biyar (N500m).

Yan sandan suna tsare da wannan dan jarida har tsayin fiye da kwana bakwai bisa tuhumarsa da cin amanar kasa, abin mamaki shine zuwa yanzu, banji karnukan dake zagin shugaba Buhari akan tuhumar da Gwamnatin ke yiwa Sowore da zargin neman juyin-juya-hali a kasar Najeriya inda ake gudanar da mulkin dimokaradiyya tsayin shekaru ashirin da suka wuce lami-lafiya.

#SenIbrahimShekarauMedia

Sakon Sanata Ibrahim Shekarau na Sabuwar Shekarar Musulinci

‎ السلام عليكم ورحمة الله تعالى و بركاته

Muna kara godiya ga Allah da ya tsawaita rayukan mu muka ga farkon wan nan shekarar ta Hijira 1441. Allah ya bamu dukkan alherin dake cikin ta, kuma ya tsare mu daga dukkan sharrin dake ciki. Allah yasa mu ga karshen shekarar lafiya. Allah ya inganta imanin mu da lafiyar mu.

‎ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻧﺖ ﺍﻷﺑﺪﻱ ﺍﻟﻘﺪﻳﻢ ﺍﻷﻭﻝ . ﻭﻋﻠﻰ ﻭﺟﻮﺩﻙ ﺍﻟﻤﻌﻮﻝ .
‎ﻭﻫﺬﺍ ﻋﺎﻡ ﺟﺪﻳﺪ ﻗﺪ ّﺃﻗﺒﻞ ﻧﺴﺄﻟﻚ ﺍﻟﻌﺼﻤﺔ ﻓﻴﻪ ﻣﻦ
‎ﺍﻟﺸﻴﻄﺎﻥ ﻭﺃﻭﻟﻴﺎﺀﻩ ﻭﺟﻨﻮﺩﻩ ﻭﺍﻟﻌﻮﻥ ﻋﻠﻰ ﻫﺬﻩ ﺍﻟﻨﻔﺲ
‎ﺍﻷﻣﺎﺭﺓ ﺑﺎﻟﺴﻮﺀ ﻭﺍﻹﺷﺘﻐﺎﻝ ﺑﻤﺎ ﻳﻘﺮﺑﻨﻲ ﺇﻟﻴﻚ ﺯﻟﻔﻰ ﻳﺎ ﺫ
‎ﺍﻟﺠﻼﻝ ﻭﺍﻹﻛﺮﺍ

‎اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحمَّد، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَميدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحمَّدٌ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَِكْتَ عَلَى إبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ

‎وكل عام وانتم بخير

Ibrahim Shekarau CON
Sanata Kano ta Tsakiya

#SenIbrahimShekarauMedia

Hijrah 1441: Jihar Osun ta bada hutu ga ma’aikata

A yau Jummah ne 1 ga watan Muharram sabuwar shekarar musulunci Hijrah 1441

Gwamnan Osun Adegboyega Oyetola tuni ya bada hutun wannan rana ga ma’aikatan Jihar domin murna zagayowar sabuwar shekarar ta musulunci, gwamnan yaba hankalin ma’aikatan suyi amfani da wannan rana wajen shagulgulan da musulmi keyi, tare da yiwa Jihar ta Osun addu’ar samun cigaba da zaman lafiya.

Gwamnan yayi wannan bayani ta hannun mai sa ido a ma’aikatar cikin gida ta Jihar Adebisi Obawale, wanda ya taya musulmin Jihar dama na duniya bakidaya murna shigowar sabuwar shekarar ta musulunci tare da yi musu fatan alkhairi da cigaba da zaman lafiya mai dorewa.

#SenIbrahimShekarauMedia

Ohanaeze sun gargadi tsagerun matasan IPOB

Kungiyar samarin dattawan Inyamurai OHANAEZE sun gargadi kungiyar tsagerun matasan Iyamurai IPOB da su guji tada kayar baya da suka shirya yi wa shugaba Buhari a kasar Japan.

Matasan na kungiyar Ohanaeze sunce yin haka zubar da mutuncin Inyamurai ne a idon duniya kuma zai sa a dinga yi musu kallon ‘yan ta’adda.

Tuni shugaban yan tada kayar baya na Inyamurai masu rajin kafa kasar Biafra Nnamdi Kanu yayi kira ga matasan kungiyar tasa ta IPOB su kaiwa shugaba Buhari hari yayin da ya ziyarci kasar Japan.

A baya-bayannan yan kungiyar ta IPOB sun kaiwa daya daga cikin dattawan Inyamurai, kuma tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa Ekweremadu hari a kasar Germany.

Idan kunne yaji jiki ya tsira.

#SenIbrahimShekarauMedia

Tirkashi: Wani aiki sai El-Rufai/Dr Hadiza Balarabe

Gwamnatin Kaduna karkashin gwamna Nasir El-Rufai zata fara biyan ma’aikatan Jihar sabon mafi karancin albashi na Naira Dubu Talatin N30,000 daga 1 ga watan Satumba na wannan shekarara.

Wannan sanarwa ta fito daga bakin mai taimakawa gwamna na masamman akan harkokin sadarwa Muyiwa Adekeye wanda ya sanar da ‘Yan jarida bayan zaman da majalisar zartarwa ta Jihar ta gudanar karkashin mataimakiyar gwamna Dr Hadiza Balarabe.

Kamar yadda ya bayyana cewa, kananan maikata zasu sami karin kashi 67% sannan matsakaitan ma’aikata masu matakin albashi na 10-14 zasu sami karin kashi 60% daga abinda suke samu a baya, don haka yayi kira ga ma’aikata su sakawa gwamnatin da alkhairin da tayi wajen zage damtse akan ayyukansu, inda yace, yanzu kudaden albashin na ma’aikata zai karu da Naira biliyon daya akan abinda gwamnatin ke biya a baya.

#SenIbrahimShekarauMedia

YABON GWANI YA ZAMA DOLE

Daga Datti Assalafiy

Masoyina Maigirma Sardaunan Kano, Sanatan Kano ta tsakiya Malam Dr Ibrahim Shekarau (Khadimul Islam)

Idan kana neman ‘dan siyasa a Nigeria da ya taimaki addinin Musulunci a fili da boye ka samu Sardaunan Kano to magana ya kare.

Idan kana neman ‘dan siyasar da yayi sanadin musuluntar da dubbannin maguzawa zuwa cikin addinin Musulunci ka samu Maigirma Sardaunan Kano magana ya kare.

Idan kana neman ‘dan siyasa mai kishin addinin Musulunci, wanda yayi ta fashi fadi har gwamnatin Nigeria ta tabbatar da jami’an tsaro na Musulunci wato rundinar Hisbah a bisa doka to shine Malam Ibrahim Shekarau.

Idan kana neman ‘dan siyasa da ya gina masallatai a arewacin Nigeria da kudanci wanda bai san adadinsu ba ka samu Maigirma Sardaunan Kano magana ya kare.

Idan kana neman kwararren dan siyasa da bai yarda da bangar siyasa ba, ka samu Maigirma Sardaunan Kano magana ya kare.

Idan kana neman ‘dan siyasa da ya gina al’umma, wanda abin hannunsa bai dameshi ba, na talakawansa ne, ka samu Sardaunan Kano magana ya kare.

Idan kana neman ‘dan siyasa da ya san darajar mutane, ya san darajar talakawanshi, yake halartan daurin aurensu da yin ta’aziyya ga talakawanshi idan ka samu Sardaunan Kano magana ya kare.

Idan kana neman ‘dan siyasa da yake katse dukkan aikin da yakeyi koda a gaban shugaban Kasa yake, da zaran lokacin Sallah yayi fita yake ya tafi Masallaci ka samu Maigirma Sardaunan Kano to magana ya kare.

Idan kana neman ‘dan siyasa daga arewa, wanda ya amsa sunan Malamin makarantan boko, ya san sirrin karatun boko, ya taka babban matsayi a karantarwa har ya zama Ministan ilmi ka samu Sardaunan Kano magana ya kare.

Idan kana neman ‘dan siyasa da ya karanta addinin Musulunci karatu na gaske, ya rubuta litattafai na addinin Musulunci ka samu Maigirma Sardaunan Kano magana ta kare.

Idan kana neman ‘dan siyasar da a duk lokacin da ya gabatar da sallah na farillah sai ya tashi yayi wa’azi irin na addinin musulunci, ya tunatar da mutane Allah (SWT) da Manzo (SAW) ka samu Sardaunan Kano to magana ya kare.

Shine Sanatan da a ranar da aka sanar da sakamako yaci zaben Sanata, masoyansa suka cika gidansa, aka sa min a waya ina sauraransu suna ta karatun Qur’ani don bayyana godiyarsu ga Allah Madaukakin Sarki, wanda wannan itace irin tarbiyyan da Maigirma Sardauna ya baiwa magoya bayanshi.

Me yasa Datti Assalafiy yake goyon bayan siyasar gidan Sardaunan Kano?
Idan kana neman dalilan to ga su can a sama, duk wanda yake da ja a kan haka to ina kalubalantarsa da kwararan hujjoji.

Shine ‘dan siyasar da a duk lokacin da na yi waya dashi, ko wani ya hadani dashi mukayi waya, ba zamu kare wayar ba sai ya saka min albarka saboda shima ‘dan albarka ne.

Maigirma Sardauna ja gaba muna binka a baya, don munsan ba zaka kaimu zuwa ga tafarkin halaka ba, sai dai hanyar tsira a duniyarmu da kuma lahirar mu.

Hoto na farko, Sardaunan Kano Khadimul Islam Malam Ibrahim Shekarau (Hafizahullah)
Hoto na biyu, Lambar yabo ne wanda dakarun social media na gidan Sardaunan Kano suka karramani dashi saboda Allah.

Yaa Allah Ka taimaki Salihin bawanKa Malam Ibrahim Shekarau, Ka daukaka mana darajarshi, Ka bashi nasara akan dukkan kyawawan manufofinshi Amin.

#SenIbrahimShekarauMedia

Kotu ta soke zaben Sanata Dino Melaye na Jihar Kogi ta Yamma

Wata kotun sauraran kararrakin zaben majalisar kasa a jihar Kogi, wacce ta kunshi alkalai uku (3) karkashin jagorancin mai shari’a A.O Chijioke ta soke zaben Sanata Dino Melaye inda tayi umarnin a sake sabon zaben sanatan mai wakiltar Kogi ta Yamma.

#SenIbrahimShekarauMedia

Sakon barka da Jummah daga Sen Ibrahim Shekarau Media

And keep yourself (O Muhammad SAW) patiently with those who call on their Lord (i.e. your companions who remember their Lord with glorification, praising in prayers, etc., and other righteous deeds, etc.) morning and afternoon, seeking His Face, and let not your eyes overlook them, desiring the pomp and glitter of the life of the world; and obey not him whose heart We have made heedless of Our Remembrance, one who follows his own lusts and whose affair (deeds) has been lost. Quran: Surah Al-Kahf Verse 28

Jummah Mubarak

#SenIbrahimShekarauMedia

Kotun sauraran koke-koken zaben gwamna a Kano zai koma Abuja da zamansa

Kotun sauraran koke-koken zaben gwamna a jihar Kano tayi barazanar komawa babban birnin tarayya Abuja da zama, matukar suka fuskanci rashin tsaro.

Mai shari’a Halima S Muhammad, tayi wannan barazana a yayi zaman sauraron shaidu masu kare tuhumar da ake musu daga hukumar zabe, inda malama Halima Sambo Hassan ma’aikaciyar hukumar zabe a karamar hukumar Ungogo ta bayyana domin bada shaidar kariya.

Ita dai malama Halima Sambo Hassan, ta hadu da kalubale ne bayan ta bada shaidar abinda tasan ya faru a inda tayi aikinta na zabe, bayan haka ne wasu suka dauki hotunanta inda suka dinga zagayawa dashi a social media ana ci mata mutunci tare da yi mata lakabi da abubuwan da bataji ba ba ta gani ba.

Lauyan hukumar zabe Adebayo Adedeji, shi ne ya koka akan haka a gaban mai shari’a, inda mai shari’a tace matukar haka zata ci gaba da faruwa, akwai alamun suma basu tsira ba, mai shari’a Halima S Muhammad tace, itace ta dage a zauna a Kano a saurari wannan shari’a saboda aba mutanen Kano damar ji da ganin yadda take kasancewa a yayin gudanar da shari’ar, maimakon a zauna a Abuja inda saidai suji a radio yadda take kasancewa.

Mai shari’a tace, indai babu tsaro a Kano to zata koma Abuja da zama, kuma ta yi kira ga hukumomi su dauki kwararan matakan tsaro kuma su binciki wannan batu na waccan mata da aka ciwa mutunci sakamakon bayyana da tayi domin bada shaida.

Shima a nasa bangaren, lauyan PDP Maliki Kuliya Umar yace, wannan abin da akayi ba daidai bane kuma shiga hurumin shari’a ne.

#SenIbrahimShekarauMedia

Bashir Ahmad ya sake komawa kan kujerar sa

Shugaban kasar Najeriya Muhammad Buhari ya sake mayar da kwararre kuma fasihin mai harkar sadarwa ta zamani a yanar gizo Bashir Ahmad kan kujerar sa ta mai taimaka masa a kafafen yada labarai na zamani.

Muna yiwa Bashir fatan alkhairi, Allah ya taya shi riko tare da fatan ya sake jajircewa wajen kawo cigaba da sauye-sauye masu ma’ana akan wannan fannin na sadarwa na zamani.

#SenIbrahimShekarauMedia

Jami’an tsaro sun cafke Wadume

Jami’an tsaro a Najeriya sun kama wani kasurgumin mai garkuwa da mutane mai suna “Wadume” shine a kwanakin baya aka kama amma a sanadiyyar kamashi da yan sanda sukayi aka sami rashin fahimta tsakaninsu da sojoji inda har akayi asarar jami’an kwararrun ‘yan sanda 3, shikuma daganan ya tsere.

Yanzu haka, an cafke wannan mutum kuma yana hannun jami’an tsaron na Najeriya.

#SenIbrahimShekarauMedia

ANA BARINMU A BAYA A HARKAR ILIMI

Tare da girmamawa a gareku.

YAU MA TALATA

An gayyace ni hira ta musamman akan batutuwa da suka shafi harkar ilimi, musamman a yankin arewa da yadda ya kamata mu kalle shi, irin yadda yafi dacewa da zamanin da muke ciki da yadda duniya ke tafiya.

Za a yi hirar a filin Zaman ‘Yan Marina “LIVE” a gidan Rediyon FM RAHAMA 97.3 a Kano. A yau Talata 10 Na safe.
Ina son in kun samu sarari ku kama tashar Rediyon FM RAHAMA ku saurara ko zamu amfana mu kara wa juna fahimta

Naku Bello Muhammad Sharada

#SenIbrahimShekarauMedia

Kotu taki amincewa ta hana Buhari rantsar da Ministoci

Wata babbar kotun tarayya dake babban birnin Abuja a ranar Litinin 19/8/2019 ta ki amincewa da wata kara da aka shigar a gabanta domin ta hana shugaban kasa Muhammad Buhari ya rantsar da Ministoci 43 da majalisar tarayya ta tantance.

Wani dan asalin garin Karu dake Abuja Mr Musa Baba-Panya, shine ya shigar da karar inda ya bukaci kotun ta hana shugaba Buhari rantsar da Ministocin nasa bisa dalilin wani hukunci da wata kotun daukaka kara tayi a ranar 15/3/2018.

Fadar shugaban kasa ta shirya rantsar da Ministocin ne ranar Laraba 21/8/2019 a fadar shugaban kasa.

#SenIbrahimShekarauMedia

Damuna Uwar Albarka

Yayin da damina tayi kyau a karkara zakaga irin wannan yanayin, ma’ana ana yin abinda ake kira “TUMU”

Shi dai “TUMU” gero ne a jikin zangarniyar sa ake yankowa daga gona kuma a hada wuta a gasa kamar yadda ake gasa masara, bayan ya gasu za’a banbareshi a murje a dinga afawa a baki ana taunawa,

“TUMU” yana da dadin ci ga gardi aci asha ruwa, wannan yana nuna cewa damina tayi kyau. Muna fatan Allah ya karawa damunar albarka ya sa muga karshenta lafiya.

Na samo wannan hoto ne daga shafin Ibrahim Z Bello Kura.

#SenIbrahimShekarauMedia

Daga Daura Mahaifar Shugaba Buhari

A yau Asabar 17/8/2019 shugaban kasar Najeriya Muhammad Buhari ya kawo karshen hutun babbar sallah da yayi a garinn haihuwar sa Daura dake Jihar Katsina inda ya shafe fiye da mako guda yana gudanar da shagulgulan sallah tare da yan’uwa da abokan arziki harma da wasu shugabannin kasashen.

Yanzu haka shugaba Buhari ya tashi zuwa babban birnin tarayya Abuja domin cigaba da aikin bautawa kasa Najeriya, muna fatan Allah ya taimaki shugabanninmu yabasu ikon aikata daidai akan talakawansu a cikin wannan mulki da Allah ya ara musu dama.

Allah ya taimaki Najeriya, ya bamu lafiya da zaman lafiya.

#SenIbrahimShekarauMedia

Sakon barka da Jummah tare da Sanata Ibrahim Shekarau

Abubuwa uku da bazaku iya dakushe haskensu ba…

1) Rana

2) Wata

3) Gaskiya

Barkanmu da wannan rana ta Jummah, Allah yabamu dukkanin alkhairan dake cikinta ya tsaremu da sharrin cikinta.

#SenIbrahimShekarauMedia

Sun rasu a hadarin mota

Inna lillahi wa inna ilaihir raji’un!

Ranar Alhamis 15/8/2019 Allah ya karbi rayukan Zainab da Muhammad Muhammad Amin Garba a wani hadarin mota da ya rutsa dasu akan hanyar Minjibir/Gezawa ta Jihar Kano.

Mahaifinsu Muhammad Amin Garba, hadimin Sanata Ibrahim Shekarau ne kuma mutumin kirki daya daga cikin malamai na a harkar fasahar na’ura mai kwakwalwa wanda ya bani gagarumar gudunmowa.

Za ayi janazarsu a ranar Jummah 16/8/2019 a gidan Isma’il Almajir dake bayan gidan Mumbayya a Gwammaja birnin Kano.

Muna addu’a Allah yai musu rahama, ya sadasu da Annabin Rahama SAAW. Allah ya ba iyayen da yan’uwa hakurin rabuwa da su.

#SenIbrahimShekarauMedia

Buhari ya hana chanja dalar Amerika domin sayo abinci daga waje

Shugaban kasar Najeriya Buhari ya takawa babban bankin kasar wato CBN birki akan bada chanjin dalar Amerika domin sayo kayan abinci daga kasashen waje zuwa Najeriya.

Ko me al’ummar Najeriya zasu ce akan haka?

#SenIbrahimShekarauMedia

PMB: zan baiwa talakawa fifiko a wannan karon

Yanzu ne talakawa zasu dandana romon dimokaradiyya a hannu na, zan baiwa talakawan fifikon kulawa a wannan zangon mulkin, zan kare hakkin su inji shugaban kasar Najeriya Buhari.

#SenIbrahimShekarauMedia

Hukumar gida yari ta koma hukumar gyarawa.

Shugaban kasar Najeriya Buhari ya sa hannu akan chanja sunan hukumar gidan yari zuwa hukumar gyarawa wacce akafi sani da Nigerian Prisons Service zuwa Nigerian Correctional Service.

Ko shakka babu wannan suna da aka chanja yafi nuna kulawa da hakkin dan Adam fiye da tsohon sunan da yake nuna garkamewa kawai ba tare da la’akari da hakkin wanda aka garkame ba.

#SenIbrahimShekarauMedia

KANO AN SAMU CIGABA

Daga Umar Faruq Muhammad:

A shekarun baya duk fadin da Kano kedashi iya Kanawan Birni ne ke shu’urin bukukuwan hawan Sallah, Mutanen mu na Kauyuka sai dai suji labari a Rediyo.

Jiya na halarci hawan Masarsutar Bichi, naga Dattawa, Samari da Yan Mata cikin Annushuwa da Sururi.

Ina da tabbacin su Salisu Shu’aibu Rano da Marakisiyya Sani Rano sun ga irin wannan sururin a Masarautar Rano.

Sani Abubakar Matankari, Umar Wada A. Karaye dasu Bello M Bbc Gaya sun fahimci hakan a Masarautun su na Karaye da Gaya.

Babu shakka Yanzu an dena ci da rabon Kanawan Kauye, za suga kwalliya zasuga mahaya Dawakai, zakuma suji Tambari da busar Algaita.

#SenIbrahimShekarauMedia

RUGA: Sanata Walid Jibrin yayi kira a rungumi shirin

Shugaban yardaddun jam’iyyar hamayya ta PDP Sen. Walid Jibrin yayi kira ga ‘yan Najeriya su rungumi shirin Gwamnatin Tarayya na Rural Grazing Areas (RUGA)

Ya bayyana haka ne a Jihar sa ta haihuwa Nassarawa, inda yace yin haka zai kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin makiyaya da manoma kuma Fulani zasu sami kulawa ta hanyar samun makarantu da asibitoci a inda aka killacesu, yin hakan zai habaka samar da yalwatar abinci, zaman lafiya da cigaban al’umma.

Sanata Walid Jibrin yace, “ni ba dan jam’iyyar APC bane, dan jam’iyyar PDP ne kuma babban jigo a cikinta, amma ina goyon bayan duk shugaban gwamnatin da zai kawo zaman lafiya da hana zubda jinin al’umma a kasa bakidaya, siyasa ta ba ta a mutu ko ayi rai bace”

Ya kara da cewa, “yanzu haka jihohin Arewacin Najeriya 12, ciki har da jihata ta Nassarawa, sun rugumi shirin inda har sun fara gudanar dashi, ina kira ga jihohin kudancin Najeriya na Inyamurai da yarabawa suma su rungumi wannan shirin, duk da dai ba dole bane, amma ya kamata mu hada kai mu yaki tashin hankali da kabilanci, da kiyayyar juna da banbancin addini a kasata Najeriya.”

Yayi kira ga Fulani su guji yin garkuwa da jama’a da fashi da makami.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito wannan labari.

#SenIbrahimShekarauMedia

Zakzaky tare da iyalinsa na kan hanyar zuwa India

Labarin dake ishemu yanzu haka na cewa, shugaban darikar shi’ah na Najeriya Zakzaky, yana kan hanyarsa ta zuwa kasar India domin neman magani tare da iyalinsa…

#SenIbrahimShekarrauMedia

AI KUNJI IRINTA

Daga Umar Faruq Muhammad:

Ina takaicin yadda aka gurbata Matasan Kano da bata sunan Jagororin mu saboda sabanin Siyasa, magana ta gaskiya banajin dadin wannan Dabi’a, shiyasa ma zakaga ko Tsula da ake amfani da ita ga tsohon Sanata ban taba rubuta ta ba, saboda a fahimtata BI’ISA ISMUL FUSUQ BA’ADAL IMAN.

Abin takaici sai gashi Jiya Jagoran Jar Hula yayi hirar Barka da Sallah, maimakon saboda muhimmancin ranar ya isar da Islahi sai yakara assasa sabon Fasadi, yakira wani Jagora da Dan Dukununu, yanzu wannan ba koyarda saka da mugun zare bane?

Ai ko MUMBARIN akayi niyyar hawa a daga kafa sai bayan bukukuwan Sallah, tunda dai a Ayyamut Tashriq muke, Ayyamul Akli wash shurbi wa DhikrulLah.

#SenIbrahimShekarauMedia

Design a site like this with WordPress.com
Get started